< Yohanna 6 >
1 Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
Emva kwalezizinto uJesu wasuka waya ngaphetsheya kolwandle lweGalili, lweTiberiyasi.
2 sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
Laselimlandela ixuku elikhulu, ngoba babebone izibonakaliso zakhe azenza kulabo abagulayo.
3 Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
UJesu wasesenyukela entabeni, wahlala phansi khona labafundi bakhe.
4 Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
Iphasika, umkhosi wamaJuda, laselisondele.
5 Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
Kwathi uJesu ephakamisa amehlo, wasebona ixuku elikhulu lisiza kuye, wathi kuFiliphu: Sizathenga ngaphi izinkwa, ukuze laba badle?
6 Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
Njalo watsho lokhu emhlola, ngoba yena wayekwazi azakwenza.
7 Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
UFiliphu wamphendula wathi: Izinkwa zabodenariyo abangamakhulu amabili zingebanele, ukuthi wonke ngamunye wabo azuze ingcosana.
8 Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
Omunye wabafundi bakhe, uAndreya umfowabo kaSimoni Petro, wathi kuye:
9 “Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
Kukhona umfanyana lapha, olezinkwa ezinhlanu zebhali lenhlanzana ezimbili; kodwa ziyini kwabanengi kangaka?
10 Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
Kodwa uJesu wathi: Hlalisani abantu phansi. Kwakukhona utshani obunengi kuleyondawo. Ngakho amadoda ahlala phansi inani lawo lalingaba zinkulungwane ezinhlanu.
11 Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
UJesu wasezithatha izinkwa, esebongile wazinika abafundi, labafundi kulabo ababehlezi phansi; ngokunjalo lenhlanzana ngangokufuna kwabo.
12 Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
Bathi sebesuthi, wathi kubafundi bakhe: Buthani imvuthu eziseleyo, ukuze kungachitheki lutho.
13 Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
Basebebutha, bagcwalisa izitsha ezilitshumi lambili ngemvuthu zezinkwa ezinhlanu zebhali, ezasalayo kulabo abadlayo.
14 Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
Kwathi lababantu bebona isimangaliso asenzileyo uJesu, bathi: Ngeqiniso lo nguye umProfethi omele ukuza emhlabeni.
15 Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
Kwathi uJesu esazi ukuthi bazakuza bambambe ngamandla, ukumbeka abe yinkosi, wabuyela futhi entabeni yena eyedwa.
16 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
Sekuhlwile, abafundi bakhe behlela elwandle,
17 inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
sebengenile emkhunjini, beza ngaphetsheya kolwandle ukuya eKapenawume. Kwasekumnyama, uJesu wayengafikanga kubo.
18 Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
Lwaseluvuka ulwandle ngoba umoya olamandla wawuvunguza.
19 Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
Sebegwedlile amastadiyu angaba ngamatshumi amabili lanhlanu kumbe amatshumi amathathu, babona uJesu ehamba phezu kolwandle, esondela emkhunjini; basebesethuka.
20 Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
Kodwa wathi kubo: Yimi, lingesabi.
21 Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
Basebevuma ukumemukela emkhunjini; njalo wahle wafika umkhumbi elizweni ababesiya kilo.
22 Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
Kusisa ixuku elalimi ngaphetsheya kolwandle, libona ukuthi kwakungela lamunye umkolo lapho ngaphandle kwalowo ababengene kuwo abafundi bakhe, lokuthi uJesu wayengangenanga emkolweni labafundi bakhe, kodwa abafundi bakhe babehambe bodwa,
23 Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
kodwa eminye imikolo evela eTiberiyasi yafika eduze lendawo lapho ababedle khona isinkwa, emva kokuthi iNkosi isibongile;
24 Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
ngakho ixuku selibonile ukuthi uJesu wayengekho lapho loba abafundi bakhe, bangena labo emikhunjini, bafika eKapenawume, bedinga uJesu.
25 Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
Bathi sebemtholile ngaphetsheya kolwandle, bathi kuye: Rabi, ufike nini lapha?
26 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
UJesu wabaphendula wathi: Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kini: Liyangidinga, kungeyisikho ukuthi labona izibonakaliso, kodwa ngoba ladla izinkwa lasutha.
27 Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
Lingasebenzeli ukudla okuphelayo, kodwa ukudla okuhlala kuze kube yimpilo elaphakade, ezalinika khona iNdodana yomuntu; ngoba yena uNkulunkulu uYise umphawulile. (aiōnios )
28 Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
Basebesithi kuye: Sizakwenzani, ukuze senze imisebenzi kaNkulunkulu?
29 Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
UJesu waphendula wathi kubo: Lo ngumsebenzi kaNkulunkulu, ukuze likholwe kulowo yena amthumileyo.
30 Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
Ngakho bathi kuye: Pho wena wenza isibonakaliso bani, ukuze sibone sikholwe kuwe? Usebenzani?
31 Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
Obaba bethu badla imana enkangala, njengokulotshiweyo ukuthi: Wabanika isinkwa esivela ezulwini ukuthi badle.
32 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
UJesu wasesithi kubo: Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kini: UMozisi kalinikanga isinkwa esivela ezulwini; kodwa uBaba ulinika isinkwa soqobo esivela ezulwini.
33 Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
Ngoba isinkwa sikaNkulunkulu singuye owehla evela ezulwini esinika impilo emhlabeni.
34 Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
Basebesithi kuye: Nkosi, sinike lesosinkwa njalonjalo.
35 Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
UJesu wasesithi kubo: Mina ngiyisinkwa sempilo; lowo oza kimi, kasoze alambe; lalowo okholwa kimi, kasoze ome lakanye.
36 Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
Kodwa ngithe kini: Lani lingibonile, kodwa kalikholwa.
37 Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
Bonke uBaba anginika bona bazakuza kimi; lozayo kimi angisoze ngimxotshele phandle.
38 Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
Ngoba ngehlile ezulwini, hatshi ukuthi ngenze intando yami, kodwa intando yalowo ongithumileyo.
39 Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
Lalokhu kuyintando kaBaba ongithumileyo, ukuze konke anginike khona, ngingalahlekelwa lutho kikho, kodwa ngikuvuse ngosuku lokucina.
40 Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
Lalokhu kuyintando yongithumileyo, ukuthi wonke obona iNdodana njalo akholwe kuyo, abe lempilo elaphakade, njalo mina ngizamvusa ngosuku lokucina. (aiōnios )
41 Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
Ngalokho amaJuda akhonona ngaye, ngoba wathi: Mina ngiyisinkwa esehla sivela ezulwini.
42 Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
Athi-ke: Lo kayisuye yini uJesu indodana kaJosefa, uyise lonina thina esibaziyo? Pho yena utsho njani, ukuthi: Ngehle ngivela ezulwini?
43 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
UJesu wasephendula wathi kuwo: Lingakhononi phakathi kwenu.
44 Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
Kakho ongeza kimi, ngaphandle kokuthi uBaba ongithumileyo amdonse, njalo mina ngizamvusa ngosuku lokucina.
45 A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
Kulotshiwe kubaprofethiukuthi: Njalo bonke bazafundiswa nguNkulunkulu. Ngakho wonke ozwileyo ngoBaba wafunda, uyeza kimi.
46 Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
Kayisikho ukuthi ukhona obone uBaba, ngaphandle kwakhe ovela kuNkulunkulu, yena umbonile uBaba.
47 Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kini: Okholwayo kimi, ulempilo elaphakade. (aiōnios )
Mina ngiyisinkwa sempilo.
49 Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
Oyihlo badla imana enkangala, futhi bafa;
50 Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
lesi yisinkwa esehla sivela ezulwini, ukuze umuntu adle okwaso angafi.
51 Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
Mina ngiyisinkwa esiphilayo, esehla sivela ezulwini; uba umuntu esidla lesisinkwa, uzaphila ephakadeni. Njalo lesinkwa mina engizasinika, siyinyama yami, mina engizayinikela impilo yomhlaba. (aiōn )
52 Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
AmaJuda asephikisana esithi: Lo angasinika njani inyama yakhe siyidle?
53 Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
Ngakho uJesu wathi kuwo: Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kini: Ngaphandle kokuthi lidle inyama yeNdodana yomuntu linathe igazi layo, kalilampilo phakathi kwenu.
54 Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
Odla inyama yami anathe igazi lami, ulempilo elaphakade, njalo mina ngizamvusa ngosuku lokucina. (aiōnios )
55 Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
Ngoba inyama yami iyikudla oqotho, legazi lami lingokunathwayo oqotho.
56 Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
Odla inyama yami anathe igazi lami, uhlala kimi, lami kuye.
57 Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
Njengalokhu uBaba ophilayo engithumile, lami ngiphila ngoBaba; ngakho ongidlayo, laye uzaphila ngami.
58 Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
Lesi yisinkwa esehla sivela ezulwini; akunjengaboyihlo abadla imana, sebafa; odla lesisinkwa, uzaphila okulaphakade. (aiōn )
59 Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
Watsho lezizinto esinagogeni efundisa eKapenawume.
60 Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
Kwathi abanengi kubafundi bakhe besizwa bathi: Lilukhuni lelilizwi; ngubani ongalizwa?
61 Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
Kodwa uJesu esazi phakathi kwakhe ukuthi abafundi bakhe bayasola ngalokhu, wathi kubo: Lokhu kuyalikhuba yini?
62 Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
Pho, lizathini uba libona iNdodana yomuntu isenyukela lapho eyayikhona kuqala?
63 Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
KunguMoya ophilisayo, inyama kayisizi lutho; amazwi mina engiwakhuluma kini, angumoya njalo ayimpilo.
64 Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
Kodwa bakhona abanye kini abangakholwayo. Ngoba uJesu wayekwazi kusukela ekuqaleni, ukuthi ngobani abangakholwayo, lokuthi ngubani ozamnikela.
65 Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
Wasesithi: Kungenxa yalokhu ngithe kini: Kakho ongeza kimi, ngaphandle kokuthi ekunikwe nguBaba.
66 Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
Kusukela lapho abanengi babafundi bakhe babuyela emuva, kababe besahamba laye.
67 Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
UJesu wasesithi kwabalitshumi lambili: Lani lithanda ukuzihambela yini?
68 Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
USimoni Petro wasemphendula wathi: Nkosi, sizakuya kubani? Amazwi empilo elaphakade akuwe, (aiōnios )
69 Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
njalo thina siyakholwa, sesisazi ukuthi wena unguKristu iNdodana kaNkulunkulu ophilayo.
70 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
UJesu wabaphendula wathi: Mina kangilikhethanga yini lina abalitshumi lambili, kodwa omunye wenu ungudiyabhola?
71 (Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)
Wayekhuluma ngoJudasi Iskariyothi kaSimoni; ngoba nguye owayezamnikela, engomunye wabalitshumi lambili.