< Yohanna 6 >

1 Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
Ensuite Jésus passa de l'autre côté de la mer de Galilée (ou de Tibériade).
2 sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
Il était suivi d'une foule immense, attirée par les miracles qu'il opérait sur les malades.
3 Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
Il gravit la montagne et y fit sa demeure ainsi que ses disciples.
4 Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
C'était aux approches de la fête juive de la Pâque.
5 Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
Ayant levé les yeux, Jésus aperçut l'immense foule qui venait à lui, et dit à Philippe: «Où achèterons-nous des pains pour leur donner à manger?»
6 Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
(Il lui parlait ainsi pour le mettre à l'épreuve; car, lui, il savait ce qu'il allait faire.)
7 Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
«Pour que chacun en eût tant soit peu, lui répondit Philippe, deux cents deniers de pains seraient insuffisants.»
8 Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
L'un des disciples (c'était. André, le, frère de Simon Pierre) dit à Jésus:
9 “Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
«Il y a ici un petit garçon qui a cinq pains d'orge et deux poissons; mais pour une pareille foule qu'est-ce que cela?» —
10 Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
«Faites asseoir ces gens», dit Jésus. En ce lieu-là, l'herbe était abondante. Les hommes s'assirent au nombre d'environ cinq mille.
11 Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
Jésus prit alors les pains, prononça l'action de grâces et les distribua à ceux qui étaient assis; il fit de même avec les poissons; ils en eurent autant qu'ils en voulaient.
12 Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
Quand tous furent rassasiés, il dit à ses disciples: «Ramassez, pour que rien ne se perde, les morceaux qui sont restés.»
13 Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
Ils les ramassèrent donc; et, avec ces morceaux des cinq pains d'orge, avec ce superflu du repas, ils remplirent douze paniers.
14 Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
Tous ces gens, s'apercevant qu'il avait fait un miracle, disaient: «C'est vraiment là le prophète qui doit venir dans le monde.»
15 Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
Sachant alors qu'ils allaient l'enlever de force pour le faire roi, Jésus se retiras de nouveau, lui seul, dans la montagne.
16 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
Quand vint le soir, ses disciples redescendirent vers la mer;
17 inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
ils montèrent dans une barque et entreprirent la traversée dans la direction de Capharnaüm. Il faisait déjà nuit, Jésus ne les avait pas encore rejoints,
18 Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
et la mer s'enflait au souffle d'un grand vent.
19 Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
Les disciples avaient parcouru environ vingt-cinq ou trente stades, quand ils aperçurent Jésus, marchant sur la mer et s'approchant de la barque. L'épouvante les saisit,
20 Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
mais Jésus leur dit: «C'est moi, soyez sans crainte.»
21 Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
Ils voulurent alors le recevoir dans la barque, et tout aussitôt elle se trouva à terre, là où ils allaient.
22 Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
Le lendemain, les multitudes, restées de l'autre côté de la mer, remarquèrent que Jésus n'était pas entré avec ses disciples dans la seule et unique barque qui fût là, et que ceux-ci étaient partis seuls.
23 Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
D'autres bateaux cependant arrivèrent de Tibériade près de l'endroit où, à la suite de l'action de grâces du Seigneur, tous avaient été nourris.
24 Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
Les multitudes, qui finirent par se convaincre que, de même que ses disciples, Jésus n'était plus là, montèrent dans ces embarcations pour aller le chercher à Capharnaüm.
25 Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
Et l'ayant en effet trouvé sur l'autre rive, elles lui demandèrent: «Rabbi, quand es-tu venu ici?»
26 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
Jésus leur répondit par ces paroles: «En vérité, en vérité, je vous le dis, vous me cherchez non pas à cause des miracles que vous avez vus, mais à cause des pains dont vous avez été nourris et rassasiés.
27 Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios g166)
Travaillez à acquérir, non l'aliment qui périt, mais l'aliment qui subsiste en vie éternelle, et que le Fils de l'homme vous donnera, le Fils de l'homme que le Père, que Dieu a marqué de son sceau.» (aiōnios g166)
28 Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
«Que devons-nous faire, lui dirent-ils, pour travailler aux oeuvres de Dieu?»
29 Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
Jésus leur répondit par ces paroles: «L'oeuvre de Dieu est d'avoir foi en celui qu'Il a envoyé.»
30 Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
Alors ils lui demandèrent: «Quel est le miracle que tu fais afin que nous le voyions et que nous ayons foi en toi? Quelle est l'oeuvre que tu accomplis?
31 Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
Nos pères ont mangé la manne dans le désert comme cela est écrit: «Il leur donna à manger un pain qui vient du ciel.»
32 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
«Le pain qui vient du ciel, leur répondit Jésus, en vérité, en vérité, je vous le dis, Moïse ne vous l'a pas donné; mais c'est mon Père qui vous donne le pain qui vient du ciel, le pain véritable.
33 Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
Le pain de Dieu est, en effet, celui qui descend du ciel et qui donne la vie au monde.»
34 Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
«Seigneur, lui demandèrent-ils, donne-nous toujours ce pain-là.»
35 Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
Jésus leur dit alors: «C'est moi qui suis le pain de la vie. Celui qui vient à moi n'aura jamais faim; celui qui croit en moi n'aura jamais soif.
36 Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
Mais je vous l'ai dit: Bien que vous m'ayez vu, vous ne croyez pas.»
37 Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
«A moi viendra tout ce que le Père me donne, et celui qui vient à moi je ne le repousserai point au dehors;
38 Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
car je suis descendu du ciel, non pour faire ma volonté, mais la volonté de Celui qui m'a envoyé.
39 Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
Or, la volonté de Celui qui m'a envoyé, c'est que je ne perde rien de ce qu'il m'a donné, mais que je ressuscite tout au dernier jour.
40 Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios g166)
Oui, la volonté de mon Père c'est que quiconque contemple le Fils et croit en lui ait la vie éternelle, et moi-même je le ressusciterai au dernier jour.» (aiōnios g166)
41 Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
Cependant les Juifs murmuraient contre cette parole de lui: «C'est moi qui suis le pain descendu du ciel.» —
42 Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
«Est-ce que ce n'est pas là Jésus, le fils de Joseph, disaient-ils, Jésus dont nous connaissons le père et la mère? Comment cet homme peut-il dire: «je suis descendu du ciel?»
43 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
Jésus leur répondit par ces paroles: «Ne murmurez pas entre vous;
44 Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
nul ne peut venir à moi, sans être attiré par le Père qui m'a envoyé, et c'est moi qui ressusciterai celui-là au dernier jour.
45 A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
Il est écrit dans les prophètes: «Ils seront tous enseignés de Dieu.» «Quiconque a entendu le Père et a appris, vient à moi.
46 Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
Non que quelqu'un ait vu le Père, sauf celui qui est de la part de Dieu, lui, il a vu le Père.»
47 Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios g166)
«En vérité, en vérité, je vous le dis, celui qui croit a la vie éternelle. (aiōnios g166)
48 Ni ne burodin rai.
Je suis, moi, le pain de la vie.
49 Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
Vos pères ont mangé la manne dans le désert; puis ils sont morts.
50 Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
Voici le pain descendant du ciel, afin qu'on en mange et qu'on ne meure points.
51 Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn g165)
Je suis, moi, le pain vivant descendu du ciel. Si quelqu'un mange de ce pain, il vivra éternellement. Et le pain que je donnerai pour la vie du monde, c'est ma chair.» (aiōn g165)
52 Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
Il y eut alors un débat entre les Juifs; ils disaient: «Comment cet homme peut-il nous donner à manger sa chair?»
53 Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
«En vérité, en vérité, je vous le dis, reprit Jésus, si vous ne mangez la chair du Fils de l'homme, et si vous ne buvez son sang, vous n'avez pas la vie en vous-mêmes.
54 Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios g166)
Qui mange ma chair et boit mon sang a la vie éternelle, et je le ressusciterai au dernier jour. (aiōnios g166)
55 Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
Car ma chair est une vraie nourriture, et mon sang est un vrai breuvage.
56 Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
Celui qui mange ma chair et boit mon sang demeure en moi et moi en lui.
57 Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
De même que Celui qui est vivant, le Père, m'a envoyé et que, moi, je vis par le Père, de même aussi celui qui me mange vivra par moi.
58 Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn g165)
Tel est le pain descendu du ciel. Il n'en est pas de lui comme de la manne dont se nourrirent vos pères, lesquels sont morts ensuite. Celui qui mange ce pain-ci vivra éternellement.» (aiōn g165)
59 Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
Telles furent les paroles de Jésus enseignant dans la synagogue à Capharnaüm.
60 Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
Après les avoir entendues, plusieurs de ses disciples dirent: «C'est dur à accepter ce qu'il dit là! Qui peut écouter ces paroles?»
61 Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
Sachant en lui-même les murmures de ses disciples à ce sujet, Jésus leur dit: «Cela vous scandalise!
62 Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
Et si vous voyiez le Fils de l'homme montant là où il était auparavant!
63 Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
C'est l'Esprit qui vivifie; la chair ne sert de rien. Les paroles que je vous ai dites sont esprit et sont vie.
64 Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
Mais il en est parmi vous quelques-uns qui, ne croient pas!» (Dès le commencement, en effet, Jésus savait quels étaient ceux qui ne croyaient point, et quel était l'homme qui le livrerait.)
65 Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
«Voilà pourquoi, ajoutait-il, je vous ai dit que nul ne peut venir à moi, à moins que cela ne lui soit donné par le Père.»
66 Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
Ce fut alors qu'un grand nombre de ses disciples se retirèrent; ils ne furent plus de sa suite; ils ne marchaient plus avec lui.
67 Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
«Et vous, voulez-vous aussi vous en aller?» dit Jésus aux douze.
68 Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios g166)
Simon Pierre lui répondit: «Seigneur, à qui irions-nous? tu as des paroles de vie éternelle, (aiōnios g166)
69 Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
et nous, nous avons cru et nous avons reconnu que tu es le Saint de Dieu.»
70 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
Jésus reprit: «N'est-ce pas moi qui vous ai choisis tous les douze? eh bien, l'un de vous est un démon!»
71 (Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)
Il parlait de Judas, fils de Simon, l'Iskariôte. C'était lui, en effet, qui devait le livrer, lui, l'un des douze.

< Yohanna 6 >