< Yohanna 5 >

1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
A potom bješe praznik Jevrejski, i iziðe Isus u Jerusalim.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
U Jerusalimu pak kod Ovèijeh vrata ima banja, koja se zove Jevrejski Vitezda, i oko nje pet pokrivenijeh trijemova,
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
U kojima ležaše mnoštvo bolesnika, slijepijeh, hromijeh, suhijeh, koji èekahu da se zaljulja voda;
4
Jer anðeo Gospodnji silažaše u odreðeno vrijeme u banju i muæaše vodu; i koji najprije ulažaše pošto se zamuti voda, ozdravljaše, makar kakva bolest da je na njemu.
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
A ondje bijaše jedan èovjek koji trideset i osam godina bješe bolestan.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
Kad vidje Isus ovoga gdje leži, i razumje da je veæ odavno bolestan, reèe mu: hoæeš li da budeš zdrav?
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
Odgovori mu bolesni: da, Gospode; ali nemam èovjeka da me spusti u banju kad se zamuti voda; a dok ja doðem drugi siðe prije mene.
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
Reèe mu Isus: ustani, uzmi odar svoj i hodi.
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
I odmah ozdravi èovjek, i uzevši odar svoj hoðaše. A taj dan bješe subota.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
Tada govorahu Jevreji onome što ozdravi: danas je subota i ne valja ti odra nositi.
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
A on im odgovori: koji me iscijeli on mi reèe: uzmi odar svoj i hodi.
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
A oni ga zapitaše: ko je taj èovjek koji ti reèe: uzmi odar svoj i hodi?
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
A iscijeljeni ne znadijaše ko je; jer se Isus ukloni, jer ljudstva mnogo bješe na mjestu.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
A potom ga naðe Isus u crkvi i reèe mu: eto si zdrav, više ne griješi, da ti ne bude gore.
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
A èovjek otide i kaza Jevrejima da je ono Isus koji ga iscijeli.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
I zato gonjahu Jevreji Isusa, i gledahu da ga ubiju, jer èinjaše to u subotu.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
A Isus im odgovaraše: otac moj doslije èini, i ja èinim.
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
I zato još više gledahu Jevreji da ga ubiju što ne samo kvaraše subotu nego i ocem svojijem nazivaše Boga i graðaše se jednak Bogu.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
A Isus odgovarajuæi reèe im: zaista, zaista vam kažem: sin ne može ništa èiniti sam od sebe nego što vidi da otac èini; jer što on èini ono i sin èini onako;
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
Jer otac sina ljubi, i sve mu pokazuje što sam èini; i pokazaæe mu veæa djela od ovijeh da se vi èudite.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
Jer kako što otac podiže mrtve i oživljuje, tako i sin koje hoæe oživljuje.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
Jer otac ne sudi nikome, nego sav sud dade sinu,
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
Da svi poštuju sina kao što oca poštuju. Ko ne poštuje sina ne poštuje oca koji ga je poslao.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
Zaista, zaista vam kažem: ko moju rijeè sluša i vjeruje onome koji je mene poslao, ima život vjeèni, i ne dolazi na sud, nego je prešao iz smrti u život. (aiōnios g166)
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Zaista, zaista vam kažem: ide èas, i veæ je nastao, kad æe mrtvi èuti glas sina Božijega, i èuvši oživljeti.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
Jer kako što otac ima život u sebi, tako dade i sinu da ima život u sebi;
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
I dade mu vlast da i sud èini, jer je sin èovjeèij.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Ne divite se ovome, jer ide èas u koji æe svi koji su u grobovima èuti glas sina Božijega,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
I iziæi æe koji su èinili dobro u vaskrsenije života, a koji su èinili zlo u vaskrsenije suda.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
Ja ne mogu ništa èiniti sam od sebe; kako èujem onako sudim, i sud je moj pravedan; jer ne tražim volje svoje nego volju oca koji me je poslao.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
Ako ja svjedoèim za sebe, svjedoèanstvo moje nije istinito.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
Ima drugi koji svjedoèi za mene; i znam da je istinito svjedoèanstvo što svjedoèi za mene.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
Vi poslaste k Jovanu, i posvjedoèi vam za istinu;
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
A ja ne primam svjedoèanstva od èovjeka, nego ovo govorim da se vi spasete.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
On bješe vidjelo koje goraše i svijetljaše, a vi se htjeste malo vremena radovati njegovu svijetljenju.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
Ali ja imam svjedoèanstvo veæe od Jovanova; jer poslovi koje mi dade otac da ih svršim, ovi poslovi koje ja radim svjedoèe za mene da me otac posla.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
I otac koji me posla sam svjedoèi za mene. Ni glasa njegova kad èuste ni lica njegova vidjeste.
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
I rijeèi njegove nemate u sebi da stoji; jer vi ne vjerujete onome koga on posla.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios g166)
Pregledajte pisma, jer vi mislite da imate u njima život vjeèni; i ona svjedoèe za mene. (aiōnios g166)
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
I neæete da doðete k meni da imate život.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
Ja ne primam slave od ljudi.
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
Nego vas poznajem da ljubavi Božije nemate u sebi.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
Ja doðoh u ime oca svojega i ne primate me; ako drugi doðe u ime svoje, njega æete primiti.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
Kako vi možete vjerovati kad primate slavu jedan od drugoga, a slave koja je od jedinoga Boga ne tražite?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
Ne mislite da æu vas tužiti ocu; ima koji vas tuži, Mojsije, u koga se vi uzdate.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
Jer da ste vjerovali Mojsiju tako biste vjerovali i meni; jer on pisa za mene.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
A kad njegovijem pismima ne vjerujete kako æete vjerovati mojijem rijeèima?

< Yohanna 5 >