< Yohanna 5 >
1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
After this there was a Festival of the Jews, and Jesus went up to Jerusalem.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
Now there is in Jerusalem near the Sheep Gate a pool, called in Hebrew 'Bethesda.' It has five arcades.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
In these there used to lie a great number of sick persons, and of people who were blind or lame or paralyzed.
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
And there was one man there who had been an invalid for thirty-eight years.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
Jesus saw him lying there, and knowing that he had been a long time in that condition, He asked him, "Do you wish to have health and strength?"
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
"Sir," replied the sufferer, "I have no one to put me into the pool when the water is moved; but while I am coming some one else steps down before me."
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
"Rise," said Jesus, "take up your mat and walk."
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
Instantly the man was restored to perfect health, and he took up his mat and began to walk.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
That day was a Sabbath. So the Jews said to the man who had been cured, "It is the Sabbath: you must not carry your mat."
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
"He who cured me," he replied, "said to me, 'Take up your mat and walk.'"
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
"Who is it," they asked, "that said to you, 'Take up your mat and walk'?"
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
But the man who had been cured did not know who it was; for Jesus had passed out unnoticed, there being a crowd in the place.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
Afterwards Jesus found him in the Temple and said to him, "You are now restored to health. Do not sin any more, or a worse thing may befall you."
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
The man went and told the Jews that it was Jesus who had restored him to health;
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
and on this account the Jews began to persecute Jesus--because He did these things on the Sabbath.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
His reply to their accusation was, "My Father works unceasingly, and so do I."
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
On this account then the Jews were all the more eager to put Him to death--because He not only broke the Sabbath, but also spoke of God as being in a special sense His Father, thus putting Himself on a level with God.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
"In most solemn truth I tell you," replied Jesus, "that the Son can do nothing of Himself--He can only do what He sees the Father doing; for whatever He does, that the Son does in like manner.
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
For the Father loves the Son and reveals to Him all that He Himself is doing. And greater deeds than these will He reveal to Him, in order that you may wonder.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
For just as the Father awakens the dead and gives them life, so the Son also gives life to whom He wills.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
The Father indeed does not judge any one, but He has entrusted all judgement to the Son,
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
that all may honour the Son even as they honour the Father. The man who withholds honour from the Son withholds honour from the Father who sent Him.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
"In most solemn truth I tell you that he who listens to my teaching and believes Him who sent me, has the Life of the Ages, and does not come under judgement, but has passed over out of death into Life. (aiōnios )
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
"In most solemn truth I tell you that a time is coming--nay, has already come--when the dead will hear the voice of the Son of God, and those who hear it will live.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
For just as the Father has life in Himself, so He has also given to the Son to have life in Himself.
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
And He has conferred on Him authority to act as Judge, because He is the Son of Man.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Wonder not at this. For a time is coming when all who are in the graves will hear His voice and will come forth--
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
they who have done what is right to the resurrection of Life, and they whose actions have been evil to the resurrection of judgement.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
"I can of my own self do nothing. As I am bidden, so I judge; and mine is a just judgement, because it is not my own will that guides me, but the will of Him who sent me.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
"If I give testimony concerning myself, my testimony cannot be accepted.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
There is Another who gives testimony concerning me, and I know that the testimony is true which He offers concerning me.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
"You sent to John, and he both was and still is a witness to the truth.
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
But the testimony on my behalf which I accept is not from man; though I say all this in order that you may be saved.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
He was the lamp that burned and shone, and for a time you were willing to be gladdened by his light.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
"But the testimony which I have is weightier than that of John; for the work the Father has assigned to me for me to bring it to completion--the very work which I am doing--affords testimony concerning me that the Father has sent me.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
And the Father who sent me, He has given testimony concerning me. None of you have ever either heard His voice or seen what He is like.
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
Nor have you His word dwelling within you, for you refuse to believe Him whom He has sent.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
"You search the Scriptures, because you suppose that in them you will find the Life of the Ages; and it is those Scriptures that yield testimony concerning me; (aiōnios )
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
and yet you are unwilling to come to me that you may have Life.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
"I do not accept glory from man,
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
but I know you well, and I know that in your hearts you do not really love God.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
I have come as my Father's representative, and you do not receive me. If some one else comes representing only himself, him you will receive.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
How is it possible for you to believe, while you receive glory from one another and have no desire for the glory that comes from the only God?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
"Do not suppose that I will accuse you to the Father. There is one who accuses you, namely Moses, on whom your hope rests.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
For if you believe Moses, you would believe me; for he wrote about me.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
But if you disbelieve his writings, how are you to believe my words?"