< Yohanna 5 >
1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
Some time later, Jesus went up to Jerusalem when the Jews were having [another] celebration.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
At one of the gates [into the city] called the Sheep Gate, there is a pool. In our language we call it Bethzatha. [Around the pool] were five open areas with roofs over them.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
Many people were lying there. They were people who were blind, lame, or paralyzed.
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
One of those who was there had been paralyzed for 38 years.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
Jesus saw him lying there and found out that the man had been like that for a long time. He said to the man, “Do you want to become well?”
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
The paralyzed man replied to him, “[Yes], sir, [I want to get well, but] there is no one to help me get down into the pool when the water is stirred {stirs}. While I am trying to get [to the pool], someone else always gets there before me.”
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
Jesus said to him, “Get up! Then pick up your mat and walk!”
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
The man immediately was healed. He picked up his mat and started walking! The day on which this happened was a Jewish day of rest.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
So the Jewish [leaders] said to the man who had been healed, “Today is (the Sabbath/our rest day), and [in our Jewish] laws [it is written that people should not work on our] ([Sabbath/rest day]), so you should not be carrying your mat!”
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
The man replied to them, “The man who healed me, he himself said to me, ‘Pick up your mat and walk!’”
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
They asked him, “Who is the man who said to you, ‘Pick it up and walk!’?”
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
But since Jesus had disappeared in the crowd [without telling the man his name], the man did not know who it was [who had healed him].
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
Later, Jesus found the man in the Temple [courtyard]. He [told the man his name, and] said to him, “Listen! You are healed! So stop sinning! If you do not stop sinning, something will happen to you that will be worse [than the illness you had before]!”
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
The man went away and told the Jewish [leaders] [SYN] that it was Jesus who had healed him.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
So the Jewish [leaders] [SYN] started to harass Jesus, because Jesus was doing these things (on the Sabbath/on the Jewish rest day).
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
Then Jesus replied to them, “My Father has always been working every day, [including] ([the Sabbath/the day of rest]), up until now. I am doing the same thing!”
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
The Jewish leaders [SYN] considered that he was disobeying their rules about (the Sabbath/the day of rest), and that by saying that God was his Father, he was making himself equal with God. And they considered that both these things were grounds for killing him. So they tried even harder to find a way to kill him.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
Jesus replied to them by saying, “You need to know this: I can do nothing by my own [authority]. I do only the [kind of] things that I see [my] Father doing. Whatever kinds of things my Father is doing, those are the things I am doing.
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
[My] Father loves me, and he shows me everything that he is doing. He will show me [the miracles] that [he wants me to do] that will be greater than the ones that [you have already seen me do], so that you may be amazed.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
[For example], just like [my] Father causes people who have died to become alive again, I will give [eternal] life to everyone that I want to.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
Furthermore, [my] Father is not the one who judges people [concerning their sins]. Instead, he has given to me the work of judging people,
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
in order that all people may honor me, just like they honor [my] Father. [My] Father [considers that] anyone who does not honor me is not honoring [him], the one who sent me.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
Listen to this carefully: Those who hear my message and believe that [God] is the one who sent me have eternal life. [God will] not (condemn them/say that he will punish them). They are no longer separated from God. Instead, they have [eternal] life. (aiōnios )
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Listen to this carefully: There will be a time when those who are (spiritually dead/separated from God) will hear the voice of me, (the Son of God/the man who is also God). In fact, it is that time already. Those who hear [and pay attention to my message] will have [eternal] life.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
[My] Father has [power to] make things live. Similarly, he has given me the [power to enable] people to live [eternally].
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
Because I am the one who came from heaven, he has given me the authority to judge people [concerning their sins].
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Do not be surprised about that, because there will be a time when all people who have died will hear my voice,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
and they will become alive again. Those who have lived good [lives] will rise [from their graves] and live forever. But those who have lived evil lives will rise, and I will (condemn them/declare that I will punish them [for their sins]).
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
I do not do anything [like that] by my own authority. I judge people only according to what I hear [my Father tell me]. I will judge people fairly, because I do not want to please only myself. Instead, I want to please [my Father], who sent me.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
If I were the [only] one to tell people about myself, [people could rightly say that] what I say is not true.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
But there is someone else who tells people about me. And I know that what he tells people about me is true.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
As for you, when you sent messengers to John [the Baptizer to ask about me], he told the truth [about me].
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
I do not [need that] people tell others [about me]. But instead, I am reminding [you about what John told people about me], in order that you will [believe it and] be saved {[God] will save you}.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
[John’s message about me] (OR, [John]) [MET] was [like] a lamp that shines brightly. For a short while you were willing to be made happy [by that message] {to let [that message] make you happy}.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
But there is something else that tells you about me. [It should prove who I am] more than what John [said about me]. The miracles [PRS] that [my] Father told me to do, the miracles that I am performing, show (OR, prove) to people that my Father sent me.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
Furthermore, [my] Father, who sent me, tells people about me. You have never heard his voice or seen him.
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
Furthermore, you have not believed in [me], the one he sent. So you have not [believed] his message in your inner beings.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
You carefully study (OR, Study) the Scriptures, because you think that by [studying] them you will [find the way to] have eternal life. And those Scriptures tell people about me! (aiōnios )
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
But you refuse (to come to me/to believe my message) in order that you may have [eternal] life.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
It does not [matter to] me whether people praise me.
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
But you [want people to praise you]. I know that within yourselves you do not love God.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
Although I have come to earth with my Father’s authority [MTY], you do not accept me. But if someone else comes with his own authority [MTY], you accept him!
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
You accept your praising each other, but you do not try to do things that will result in God himself praising you. So (there is no way you can believe [in me]!/how can you believe [my message]?) [RHQ]
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
But do not think that I am the one who will accuse you while [my] Father is listening! No, it is Moses who will accuse you! You thought that he would [defend you].
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
Moses wrote about me, so if you had believed what he [wrote], you would have believed what I [said]
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
But because you did not believe what he wrote [about me], (you will certainly not believe what I say!/how will you believe what I say?) [RHQ]”