< Yohanna 5 >
1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
After these things there was the feast of the Jews, and Jesus went up to Jerusalem.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
Now there is at Jerusalem, by the sheep-gate, a pool, which is called in Hebrew Bethzatha, having five porches.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
In these were lying a multitude of diseased persons, blind, lame, withered.
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
And a certain man was there, who had had his infirmity thirty-eight years.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
Jesus saw this man lying there, and knowing that he had been for a long time diseased, saith to him, Dost thou wish to be made well?
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
The diseased man answered him, Sir, I have no man, when the water is troubled, to put me into the pool; but while I am coming, another goeth down before me.
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
Jesus saith to him, Rise, take up thy bed, and walk.
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
And immediately the man was made well, and took up his bed, and walked. And that day was the sabbath.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
The Jews therefore said to him that was cured, It is the sabbath; and it is not lawful for thee to take up the bed.
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
He answered them, He that made me well, the same said to me, Take up thy bed, and walk. T
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
hey asked him, Who is the man that said to thee, Take up, and walk?
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
But the diseased man knew not who it was; for Jesus had withdrawn himself, there being a crowd in the place.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
Afterwards Jesus found him in the temple, and said to him, Behold, thou art made well; sin no more, lest something worse befall thee.
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
The man went away, and told the Jews that it was Jesus who had made him well.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
And on this account the Jews persecuted Jesus, because he did these things on the sabbath.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
But he answered them, My Father is working up to this time, and I work.
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
On this account the Jews sought the more to kill him, because he not only broke the sabbath, but also said that God was his own Father, making himself equal with God.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
Then answered Jesus and said to them, Truly, truly do I say to you, The Son can do nothing of himself, but what he seeth the Father doing; for whatever He doeth, these things the Son also doeth in like manner;
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
for the Father loveth the Son, and showeth him all things which he himself doeth; and greater works than these will he show him, so that ye will wonder.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
For as the Father raiseth up the dead, and giveth them life, so the Son also giveth life to whom he will.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
For neither doth the Father judge any one, but hath committed all judgment to the Son;
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
that all may honor the Son, as they honor the Father. He that honoreth not the Son, honoreth not the Father, who sent him.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
Truly, truly do I say to you, He that heareth my word, and believeth him that sent me, hath everlasting life, and cometh not into condemnation, but hath passed out of death into life. (aiōnios )
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Truly, truly do I say to you, The hour is coming and now is, when the dead will hear the voice of the Son of God; and they that hear will live.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
For as the Father hath life in himself, so did he give to the Son also to have life in himself.
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
And he gave him authority to execute judgment, because he is a son of man.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Marvel not at this; for the hour is coming, in which all that are in the tombs will hear his voice,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
and will come forth, they that have done good, to a resurrection of life; they that have done evil, to a resurrection of condemnation.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
I can of myself do nothing. As I hear, I judge; and my judgment is just, because I seek not my own will, but the will of him that sent me.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
If I bear witness of myself, my witness is not true.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
There is another who beareth witness of me; and ye know that the witness which he witnesseth of me is true.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
Ye have sent to John, and he hath borne witness to the truth.
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
But the testimony which I receive is not from man; but these things I say, that ye may be saved.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
He was the burning and shining lamp: and ye were willing for a season to rejoice in his light.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
But the testimony which I have, is greater than that of John; for the works which the Father hath given me to perform, the works themselves which I do, bear witness of me, that the Father hath sent me.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
And the Father who sent me, he hath borne witness of me. Ye have neither heard his voice at any time, nor seen his form.
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
And ye have not his word abiding in you; for whom he sent, him ye believe not.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
Ye search the Scriptures, because ye yourselves think that in them ye have everlasting life; and it is they which testify of me; (aiōnios )
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
and ye are not willing to come to me, that ye may have life.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
I receive not honor from men;
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
but I know you, that ye have not the love of God in you.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
I have come in my Father's name, and ye receive me not; if another come in his own name, him ye will receive.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
How can ye believe while ye receive honor from one another, and seek not the honor that is from him who alone is God?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
Do not think that I shall accuse you to the Father; there is one that accuseth you, even Moses, in whom ye have placed your hope.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
For if ye believed Moses, ye would believe me; for he wrote of me.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
But if ye do not believe his writings, how will ye believe my words?