< Yohanna 5 >

1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
After these things, there was a Jewish festival, and Jesus went up to Jerusalem.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
Now in Jerusalem by the sheep area there is a pool, which is called in Hebrew, "Beth Hesda," having five porches.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
In these lay a multitude of those who were sick, blind, lame, or paralyzed.
4
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
A certain man was there, who had been sick for thirty-eight years.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
When Jesus saw him lying there, and knew that he had been sick for a long time, he asked him, "Do you want to be made well?"
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
The sick man answered him, "Sir, I have no one to put me into the pool when the water is stirred up, but while I am on my way, someone else steps down ahead of me."
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
Jesus said to him, "Arise, take up your mat, and walk."
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
Immediately, the man was made well, and took up his mat and walked. Now it was the Sabbath on that day.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
So the Jewish leaders said to him who was cured, "It is the Sabbath. It is not lawful for you to carry the mat."
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
But he answered them, "The one who made me well, that one said to me, 'Take up your mat, and walk.'"
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
Then they asked him, "Who is the man who said to you to pick it up and walk?"
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
But the one who was healed did not know who it was, for Jesus had withdrawn, a crowd being in the place.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
Afterward Jesus found him in the temple, and said to him, "See, you are made well. Sin no more, so that nothing worse happens to you."
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
The man went away, and told the Jewish leaders that it was Jesus who had made him well.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
For this cause the Jewish leaders persecuted Jesus, because he did these things on the Sabbath.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
But he answered them, "My Father is still working, so I am working, too."
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
For this cause therefore the Jewish leaders sought all the more to kill him, because he not only broke the Sabbath, but also called God his own Father, making himself equal with God.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
Jesus therefore answered them, "Truly, truly, I tell you, the Son can do nothing of himself, but what he sees the Father doing. For whatever things he does, these the Son also does likewise.
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
For the Father loves the Son, and shows him all things that he himself does. He will show him greater works than these, so that you may marvel.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
For as the Father raises the dead and gives them life, even so the Son also gives life to whom he desires.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
For the Father judges no one, but he has given all judgment to the Son,
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
that all may honor the Son, even as they honor the Father. Whoever does not honor the Son does not honor the Father who sent him.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
"Truly, truly, I tell you, he who hears my word, and believes him who sent me, has everlasting life, and does not come into judgment, but has passed out of death into life. (aiōnios g166)
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Truly, truly, I tell you, the hour comes, and now is, when the dead will hear the Son of God's voice; and those who hear will live.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
For as the Father has life in himself, even so he gave to the Son also to have life in himself.
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
He also gave him authority to execute judgment, because he is the Son of Man.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Do not be amazed at this, for the hour comes, in which all that are in the tombs will hear his voice,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
and will come out; those who have done good, to the resurrection of life; and those who have done evil, to the resurrection of judgment.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
I can of myself do nothing. As I hear, I judge, and my judgment is righteous; because I do not seek my own will, but the will of the One who sent me.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
"If I testify about myself, my witness is not valid.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
It is another who testifies about me. I know that the testimony which he testifies about me is true.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
You have sent to John, and he has testified to the truth.
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
But the testimony which I receive is not from man. However, I say these things that you may be saved.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
He was the burning and shining lamp, and you were willing to rejoice for a while in his light.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
But the testimony which I have is greater than that of John, for the works which the Father gave me to accomplish, the very works that I do, testify about me, that the Father has sent me.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
The Father himself, who sent me, has testified about me. You have neither heard his voice at any time, nor seen his form.
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
You do not have his word living in you; because you do not believe him whom he sent.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios g166)
You search the Scriptures, because you think that in them you have everlasting life; and these are they which testify about me. (aiōnios g166)
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
But you are unwilling to come to me so that you may have life.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
I do not receive glory from people.
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
But I know you, that you do not have God's love in yourselves.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
I have come in my Father's name, and you do not receive me. If another comes in his own name, you will receive him.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
How can you believe, who receive glory from one another, and you do not seek the glory that comes from the only God?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
"Do not think that I will accuse you to the Father. There is one who accuses you, even Moses, on whom you have set your hope.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
For if you believed Moses, you would believe me; for he wrote about me.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
But if you do not believe his writings, how will you believe my words?"

< Yohanna 5 >