< Yohanna 5 >
1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
After these things was the feast of the Jews; and Jesus went up into Jerusalem.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
And there is a pool at the sheep-market, called in Hebrew Bethzatha, having five porches.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
In them a multitude of the sick, blind, lame, withered, were lying down.
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
And a certain man was there, being thirty-eight years in his infirmity;
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
Jesus seeing him lying down, and knowing that he already has much time, says to him; Do you wish to be whole?
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
The sick man responded to Him, Lord, I have no man that may put me in the pool, when the water may be troubled: and while I come, another goes down before me.
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
And Jesus says to him, Arise, take thy bed, and walk about.
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
And the man was made whole, and he took up his bed and continued to walk about. And it was the Sabbath on that day.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
Then the Jews were saying to the healed man, It is the Sabbath, and it is not lawful for thee to carry thy bed.
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
He responded to them, the one having made me whole, He said to me, Take thy bed, and walk about.
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
They asked him, Who is the man who said to thee, Take thy bed, and walk about?
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
And the sick man did not know who He is: for Jesus went out, the crowd being in the place.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
And after these things, Jesus finds him in the temple, and said to him, Behold, thou hast been made whole: sin no more, lest something worse may come on thee.
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
And the man departed, and said to the Jews, that Jesus is the one having made him whole.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
And on account of this the Jews continued to persecute Jesus, because He was doing these things on the Sabbath.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
And He responded to them, My Father worketh until now, and I work.
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
Therefore the Jews the more sought to kill Him, because He not only broke the Sabbath, but said that God was His Father, making himself equal to God.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
Then Jesus responded and said to them, Truly, truly, I say unto you, The Son is not able to do anything Himself, unless He may see the Father doing it: for whatsoever He may do, the Son likewise also doeth the same.
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
For the Father loveth the Son, and showeth Him all things which He doeth; and will show Him greater things than these, in order that you may be astonished.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
For as the Father raiseth up the dead and createth life in them, so the Son also createth life in whom He will.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
For the Father judgeth no one, for He hath given all judgment to the Son;
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
in order that all may honor the Son, as they may honor the Father. He that honoreth not the Son honoreth not the Father who sent Him.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
Truly, truly, I say unto you, that every one hearing my word, and believing on Him that sent me hath eternal life, and doth not come into judgment, but has passed out of death into life. (aiōnios )
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Truly, truly, I say unto you, that the hour cometh and now is, when the dead will hear the voice of the Son of God; and having heard will live.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
For as the Father hath life in Himself, so also He has given to His Son to have life also in Himself.
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
And He hath given Him authority to execute the judgment, because He is the Son of man.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Do not be astonished at this: because the hour cometh, in which all who are in their graves will hear His voice,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
and come forth; those having done good, unto the resurrection of life; and those having done evil, unto the resurrection of judgment.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
I am not able to do anything of myself: as I hear, I judge: and my judgment is righteous; because I do not seek my own will, but the will of the One having sent me.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
If I testify concerning myself, my testimony is not true.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
There is another who testifieth concerning me; and you know that the testimony which He testifies concerning me is true.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
You sent to John, and he witnessed to the truth:
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
but I do not receive the witness with man: but I speak these things that you may be saved.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
He was a bright and shining light: and you were willing to rejoice for an hour in that light.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
But I have a testimony greater than that of John: for the works that the Father hath given me that I may perfect them, these works which I do, testify concerning me, that the Father hath sent me.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
And the Father having sent me, He hath testified concerning me: never have you heard His voice, neither have you seen His face:
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
and you have not His word abiding in you: because you do not believe Him whom He has sent.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
Search the Scriptures, because in them ye think ye have eternal life; and they are they which testify concerning me; (aiōnios )
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
and you do not wish to come unto me, in order that you may have life.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
I do not receive glory with men;
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
but I know you that you have not the love of God in you.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
I have come in the name of my Father, and you do not receive me: if another may come in his own name, you will receive him.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
How are you able to believe, receiving glory from one another, and do not seek the glory which is with God only?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
Do not think that I will accuse you to the Father; there is one accusing you, in whom you have hoped.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
For if you were believing Moses, you were believing me; for he wrote concerning me.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
For if you do not believe his writings, how will you believe my words?