< Yohanna 5 >

1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
After this was the feast of the Jews; and Jesus went up to Jerusalem.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
Now there is in Jerusalem, near the sheep-gate, a pool, called, in the Hebrew tongue, Bethesda, with five porches.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
In these lay a great multitude of sick persons, blind, lame, withered, who waited for the moving of the water.
4
For an angel went down at a certain season into the pool, and stirred the water. Then he who entered first after the motion of the water, was cured of whatever disease he had.
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
And a certain man was there, who had been sick thirty-eight years.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
When Jesus saw him lying, and knew that he had been already a long time in that condition, he said to him: Do you wish to be restored to health?
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
The sick man answered him: Sir, I have no man to put me into the pool when the water is stirred; but while I am coming, another goes down before me.
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
Jesus said to him: Arise, take up your bed and walk.
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
And the man was immediately restored to health; and he took up his bed and walked. And that day was the sabbath.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
The Jews, therefore, said to him that was cured: It is the sabbath; it is not lawful for you to carry your bed.
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
He answered them: He that restored me to health said to me, Take up your bed and walk.
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
Then they asked him: Who is he that said to you, Take up your bed and walk?
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
But he that had been restored to health knew not who he was; for Jesus had withdrawn himself, because a multitude was in the place.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
After this Jesus found him in the temple, and said to him: Behold, you have been restored to health; sin no more, lest some worse thing befall you.
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
The man departed, and told the Jews that it was Jesus that had restored him to health.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
And for this reason did the Jews persecute Jesus, and seek to kill him, because he had done these things on the sabbath.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
But Jesus answered them: My Father works till now, and I also work.
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
For this reason, therefore, the Jews sought the more to kill him, because he had not only broken the sabbath, but also said that God was his own father, making himself equal with God.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
Then Jesus answered and said to them: Verily, verily I say to you, The Son can do nothing of himself, but what he sees the Father do; for whatever things he does, these also the Son does in like manner.
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
For the Father loves the Son, and shows him all things that he himself does; and he will show him greater works than these, that you may be astonished.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
For as the Father raises the dead, and makes them alive, so also the Son makes alive whom he will.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
For the Father judges no one, but has given all judicial authority to the Son;
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
that all may honor the Son, as they honor the Father. He that honors not the Son, honors not the Father who sent him.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
Verily, verily I say to you, He that hears my word, and believes on him that sent me, has eternal life, and comes not into condemnation, but has passed from death into life. (aiōnios g166)
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Verily, verily I say to you, The hour is coming, and now is, when the dead shall hear the voice of the Son of God, and those who hear, shall live.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
For as the Father has life in himself, so has he given to the Son also to have life in himself;
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
and he has given him authority to execute judgment also, because he is the Son of man.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Be not astonished at this; for the hour is coming in which all that are in the graves shall hear his voice,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
and shall come forth; those who have done good, to the resurrection of life, and those who have done evil, to the resurrection of condemnation.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
I can of myself do nothing. As I hear, I judge; and my judgment is just, because I seek not my own will, but the will of him that sent me.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
If I testify concerning myself, my testimony is not worthy of credit.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
There is another that testifies concerning me, and I know that the testimony which he testifies concerning me is worthy of credit.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
You sent to John, and he bore testimony to the truth.
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
But I receive not testimony from man; yet I say these things that you may be saved.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
He was the burning and shining lamp; and you were willing, for a time, to rejoice in his light.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
But I have testimony greater than that of John; for the works which the Father has given me to finish, these very works which I do, testify concerning me, that the Father has sent me.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
And the Father, who sent me, has testified concerning me. You have, neither heard his voice at any time, nor seen his shape.
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
And his word you have not remaining in you; for whom he has sent, him you believe not.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios g166)
You search the scriptures, because in them you think you have eternal life; and these are they which testify concerning me: (aiōnios g166)
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
and yet you refuse to come to me, that you may have life.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
I receive not honor from men.
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
But I know you, that you have not the love of God in you.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
I have come in my Father’s name, and you receive me not; if another should come in his own name, him you would receive.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
How can you believe who receive honor one from another, and seek not the honor that comes from God alone?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
Think not that I will accuse you to the Father: there is one that accuses you, Moses, in whom you trust.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
For if you had believed Moses, you would have believed me; for he wrote of me.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
But if you believe not his writings, how shall you believe my words?

< Yohanna 5 >