< Yohanna 5 >
1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
Derefter var det Jødernes Højtid, og Jesus gik op til Jerusalem.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
Men der er i Jerusalem ved Faareporten en Dam, som paa Hebraisk kaldes Bethesda, og den har fem Søjlegange.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
I dem laa der en Mængde syge, blinde, lamme, visne, [som ventede paa, at Vandet skulde røres.
Thi paa visse Tider for en Engel ned i Dammen og oprørte Vandet. Den, som da, efter at Vandet var blevet oprørt, steg først ned, blev rask, hvilken Sygdom han end led af.]
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
Men der var en Mand, som havde været syg i otte og tredive Aar.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
Da Jesus saa ham ligge der og vidste, at han allerede havde ligget i lang Tid, sagde han til ham: „Vil du blive rask?”
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
Den syge svarede ham: „Herre! jeg har ingen, som kan bringe mig ned i Dammen, naar Vandet bliver oprørt; men naar jeg kommer, stiger en anden ned før mig.”
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
Jesus siger til ham: „Staa op, tag din Seng og gaa!”
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
Og straks blev Manden rask, og han tog sin Seng og gik. Men det var Sabbat paa den Dag;
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
derfor sagde Jøderne til ham, som var bleven helbredet: „Det er Sabbat; og det er dig ikke tilladt at bære Sengen.”
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
Han svarede dem: „Den, som gjorde mig rask, han sagde til mig: Tag din Seng og gaa!”
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
Da spurgte de ham: „Hvem er det Menneske, som sagde til dig: Tag din Seng og gaa?”
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
Men han, som var bleven helbredet, vidste ikke, hvem det var; thi Jesus havde unddraget sig, da der var mange Mennesker paa Stedet.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
Derefter finder Jesus ham i Helligdommen, og han sagde til ham: „Se, du er bleven rask; synd ikke mere, for at ikke noget værre skal times dig!”
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
Manden gik bort og sagde til Jøderne, at det var Jesus, som havde gjort ham rask.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
Og derfor forfulgte Jøderne Jesus, fordi han havde gjort dette paa en Sabbat.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
Men Jesus svarede dem: „Min Fader arbejder indtil nu; ogsaa jeg arbejder.”
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
Derfor tragtede da Jøderne end mere efter at slaa ham ihjel, fordi han ikke alene brød Sabbaten, men ogsaa kaldte Gud sin egen Fader og gjorde sig selv Gud lig.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
Saa svarede Jesus og sagde til dem: „Sandelig, sandelig, siger jeg eder, Sønnen kan slet intet gøre af sig selv, uden hvad han ser Faderen gøre; thi hvad han gør, det gør ogsaa Sønnen ligesaa.
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
Thi Faderen elsker Sønnen og viser ham alt det, han selv gør, og han skal vise ham større Gerninger end disse, for at I skulle undre eder.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
Thi ligesom Faderen oprejser de døde og gør levende, saaledes gør ogsaa Sønnen levende, hvem han vil.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
Thi heller ikke dømmer Faderen nogen, men har givet Sønnen hele Dommen,
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
for at alle skulle ære Sønnen, ligesom de ære Faderen. Den, som ikke ærer Sønnen, ærer ikke Faderen, som udsendte ham.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
Sandelig, sandelig, siger jeg eder, den, som hører mit Ord og tror den, som sendte mig, har et evigt Liv og kommer ikke til Dom, men er gaaet over fra Døden til Livet. (aiōnios )
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Sandelig, sandelig, siger jeg eder, den Time kommer, ja den er nu, da de døde skulle høre Guds Søns Røst, og de, som høre den, skulle leve.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
Thi ligesom Faderen har Liv i sig selv, saaledes har han ogsaa givet Sønnen at have Liv i sig selv.
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
Og han har givet ham Magt til at holde Dom, efterdi han er Menneskesøn.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Undrer eder ikke herover; thi den Time kommer, paa hvilken alle de, som ere i Gravene, skulle høre hans Røst,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
og de skulle gaa frem, de, som have gjort det gode, til Livets Opstandelse, men de, som have gjort det onde, til Dommens Opstandelse.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
Jeg kan slet intet gøre af mig selv; saaledes som jeg hører, dømmer jeg, og min Dom er retfærdig; thi jeg søger ikke min Villie, men hans Villie, som sendte mig.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
Dersom jeg vidner om mig selv, er mit Vidnesbyrd ikke sandt.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
Det er en anden, som vidner om mig, og jeg ved, at det Vidnesbyrd er sandt, som han vidner om mig.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
I have sendt Bud til Johannes, og han har vidnet for Sandheden.
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
Dog, jeg henter ikke Vidnesbyrdet fra et Menneske; men dette siger jeg, for at I skulle frelses.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
Han var det brændende og skinnende Lys, og I have til en Tid villet fryde eder ved hans Lys.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
Men det Vidnesbyrd, som jeg har, er større end Johannes's; thi de Gerninger, som Faderen har givet mig at fuldbyrde, selve de Gerninger, som jeg gør, vidne om mig, at Faderen har udsendt mig.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
Og Faderen, som sendte mig, han har vidnet om mig. I have aldrig hverken hørt hans Røst eller set hans Skikkelse,
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
og hans Ord have I ikke blivende i eder; thi den, som han udsendte, ham tro I ikke.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
I ransage Skrifterne, fordi I mene i dem at have evigt Liv; og det er dem, som vidne om mig. (aiōnios )
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
Og I ville ikke komme til mig, for at I kunne have Liv.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
Jeg tager ikke Ære af Mennesker;
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
men jeg kender eder, at I have ikke Guds Kærlighed i eder.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
Jeg er kommen i min Faders Navn, og I modtage mig ikke; dersom en anden kommer i sit eget Navn, ham ville I modtage.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
Hvorledes kunne I tro, I, som tage Ære af hverandre, og den Ære, som er fra den eneste Gud, søge I ikke?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
Tænker ikke, at jeg vil anklage eder for Faderen; der er en, som anklager eder, Moses, til hvem I have sat eders Haab.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
Thi dersom I troede Moses, troede I mig; thi han har skrevet om mig.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
Men tro I ikke hans Skrifter, hvorledes skulle I da tro mine Ord?”