< Yohanna 4 >

1 Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
And Jesus knew, that the Pharisees had heard; that he made many disciples, and baptized more than John.
2 ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
Yet Jesus himself did not baptize but his disciples.
3 Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
And he left Judaea, and went again into Galilee.
4 To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
And in going, he had occasion to pass through the midst of the Samaritans.
5 Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
And he came to a city of the Samaritans called Sychar, near the field which Jacob gave to his son Joseph.
6 Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
And Jacob's well of water was there. And Jesus was weary with the toil of travelling, and seated himself by the well: and it was at the sixth hour.
7 Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
And a woman from Samaria came to draw water. And Jesus said to her: Give me water to drink.
8 (Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
And his disciples had gone to the city, to buy themselves food.
9 Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
The Samaritan woman said to him: How dost thou, a Jew, ask drink of me, who am a Samaritan woman? For the Jews have no familiarity with Samaritans.
10 Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
Jesus replied and said to her: If thou hadst known the gift of God, and who it is that saith to thee, Give me to drink, thou wouldest have asked of him, and he would have given thee living waters.
11 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
The woman said to him: My lord, thou hast no bucket, and the well is deep.; how hast thou living waters?
12 Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
Art thou greater than our father Jacob, who gave us this well, and drank from it himself, and his children, and his flocks?
13 Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
Jesus replied and said to her: Whoever shall drink of these waters, will thirst again;
14 amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
but whoever shall drink of the waters which I shall give him, will not thirst for ever; but the waters, which I shall give him, will be in him a fountain of waters, springing up unto life eternal. (aiōn g165, aiōnios g166)
15 Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
The woman said to him: My lord, give me of these waters, that I may not thirst again, and may not come to draw from here.
16 Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
Jesus said to her: Go, call thy husband, and come hither.
17 Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
She said to him: I have no husband. Jesus said to her: Thou hast well said, I have no husband;
18 Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
for thou hast had five husbands, and he whom thou now hast, is not thy husband. In this thou didst speak truly.
19 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
The woman said to him: My lord, I perceive thou art a prophet.
20 Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
Our fathers worshipped in this mountain; but ye say, that in Jerusalem is the place where it is proper to worship.
21 Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
Jesus said to her: Woman, believe me, the hour cometh, when neither in this mountain, nor in Jerusalem, ye will worship the Father.
22 Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
Ye worship, ye know not what; but we worship what we know; for life is from the Jews.
23 Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
But the hour cometh, and now is, when the true worshippers will worship the Father in spirit and in truth; for the Father requireth that worshippers be such.
24 Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
For God is a Spirit; and they that worship him, should worship in spirit and in truth.
25 Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
The woman said to him: I know that Messiah will come; and when he cometh, he will teach us every thing.
26 Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
Jesus said to her: I, who talk with thee, am he.
27 Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
And while he was speaking, his disciples came. And they wondered that he would converse with the woman; yet no one said, What seekest thou? or, Why talkest thou with her?
28 Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
And the woman left her water-pot, and went to the city, and said to the people:
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
Come, see a man that told me every thing I ever did: is not this the Messiah?
30 Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
And the people went out of the city, and came to him.
31 Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
In the mean time, his disciples entreated him, and said to him: Our Rabbi, eat.
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
But he said to them: I have food to eat, of which ye are ignorant.
33 Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
The disciples said among themselves: Hath any one brought him something to eat?
34 Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
Jesus said to them: My food is to do the pleasure of him that sent me, and to accomplish his work.
35 Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
Do ye not say, that after four months cometh the harvest? Behold, I say to you, and lift up your eyes, and look upon the grounds, that they are white, and have already come to the harvest.
36 Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios g166)
And he that reapeth, receiveth wages, and gathereth fruits unto life eternal; and the sower and the reaper equally rejoice. (aiōnios g166)
37 Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
For in this, is the proverb true, that one is the sower, and another the reaper.
38 Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
I sent you to reap that, on which ye labored not: for others toiled, and ye entered into their labor.
39 Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
And many Samaritans of that city believed on him, because of the discourse of the woman, who testified, He told me all that I ever did.
40 To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
And when these Samaritans came to him, they requested him to tarry with them; and he remained with them two days.
41 Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
And many believed on him, because of his discourse.
42 Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
And they said to the woman: Henceforth we believe in him, not on account of thy word; for we have heard him ourselves, and we know that he truly is the Messiah, the Life-Giver of the world.
43 Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
And after two days Jesus departed from there and went into Galilee.
44 (To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
For Jesus himself testified, that a prophet is not honored in his own city.
45 Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
And when he came to Galilee, the Galileans received him, having seen all the signs which he wrought in Jerusalem at the feast, for they too had gone to the feast.
46 Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
And Jesus came again to Cana of Galilee, where he made the water wine. And there was at Capernaum a king's servant, whose son was sick.
47 Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
He heard that Jesus had come from Judaea to Galilee; and he went to him, and besought him that he would come down and heal his son; for he was near dying.
48 Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
Jesus said to him: Unless ye see signs and wonders, ye will not believe.
49 Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
The king's servant said to him: My lord, come down, before the child dieth.
50 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
Jesus said to him: Go, thy son liveth. And the man believed the word which Jesus spake to him, and went away.
51 Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
And as he was going down, his servants met him, and informed him and said to him: Thy son liveth.
52 Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
And he asked them, at what time he recovered. And they said to him: Yesterday, at the seventh hour the fever left him.
53 Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
And his father knew, that it was at the hour in which Jesus said to him, Thy son liveth. And he believed, and all his house.
54 Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.
This again was the second sign that Jesus wrought, when he came from Judaea to Galilee.

< Yohanna 4 >