< Yohanna 4 >
1 Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
When therefore the LORD knew how the Pharisees had heard that Jesus made and baptized more disciples than John,
2 ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
(Though Jesus himself baptized not, but his disciples, )
3 Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
He left Judaea, and departed again into Galilee.
4 To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
And he must essentially go through Samaria.
5 Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
Then comes he to a city of Samaria, which is called Sychar, near to the parcel of ground that Jacob gave to his son Joseph.
6 Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
Now Jacob's well was there. Jesus therefore, being wearied with his journey, sat thus on the well: and it was about the sixth hour.
7 Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
There comes a woman of Samaria to draw water: Jesus says unto her, Give me to drink.
8 (Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
(For his disciples were gone away unto the city to buy food.)
9 Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
Then says the woman of Samaria unto him, How is it that you, being a Jew, ask drink of me, which am a woman of Samaria? for the Jews have no dealings with the Samaritans.
10 Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
Jesus answered and said unto her, If you knew the gift of God, and who it is that says to you, Give me to drink; you would have asked of him, and he would have given you living water.
11 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
The woman says unto him, Sir, you have nothing to draw with, and the well is deep: from whence then have you that living water?
12 Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
Are you greater than our father Jacob, which gave us the well, and drank thereof himself, and his children, and his cattle?
13 Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
Jesus answered and said unto her, Whosoever drinks of this water shall thirst again:
14 amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn , aiōnios )
But whosoever drinks of the water that I shall give him shall never thirst; but the water that I shall give him shall be in him a well of water springing up into everlasting life. (aiōn , aiōnios )
15 Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
The woman says unto him, Sir, give me this water, that I thirst not, neither come here to draw.
16 Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
Jesus says unto her, Go, call your husband, and come here.
17 Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
The woman answered and said, I have no husband. Jesus said unto her, You have well said, I have no husband:
18 Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
For you have had five husbands; and he whom you now have is not your husband: in that said you truly.
19 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
The woman says unto him, Sir, I perceive that you are a prophet.
20 Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
Our fathers worshipped in this mountain; and all of you say, that in Jerusalem is the place where men ought to worship.
21 Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
Jesus says unto her, Woman, believe me, the hour comes, when all of you shall neither in this mountain, nor yet at Jerusalem, worship the Father.
22 Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
All of you worship all of you know not what: we know what we worship: for salvation is of the Jews.
23 Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
But the hour comes, and now is, when the true worshippers shall worship the Father in spirit (pneuma) and in truth: for the Father seeks such to worship him.
24 Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
God is a Spirit: (pneuma) and they that worship him must worship him in spirit (pneuma) and in truth.
25 Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
The woman says unto him, I know that Messiah comes, which is called Christ: when he has come, he will tell us all things.
26 Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
Jesus says unto her, I that speak unto you am he.
27 Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
And upon this came his disciples, and marvelled that he talked with the woman: yet no man said, What seek you? or, Why talk you with her?
28 Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
The woman then left her water pot, and went her way into the city, and says to the men,
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
Come, see a man, which told me all things that ever I did: is not this the Christ?
30 Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
Then they went out of the city, and came unto him.
31 Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
In the mean while his disciples prayed him, saying, Master, eat.
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
But he said unto them, I have food to eat that all of you know not of.
33 Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
Therefore said the disciples one to another, Has any man brought him ought to eat?
34 Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
Jesus says unto them, My food is to do the will of him that sent me, and to finish his work.
35 Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
Say not all of you, There are yet four months, and then comes harvest? behold, I say unto you, Lift up your eyes, and look on the fields; for they are white already to harvest.
36 Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios )
And he that reaps receives wages, and gathers fruit unto life eternal: that both he that sows and he that reaps may rejoice together. (aiōnios )
37 Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
And herein is that saying (logos) true, One sows, and another reaps.
38 Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
I sent you to reap that whereon all of you bestowed no labour: other men laboured, and all of you are entered into their labours.
39 Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
And many of the Samaritans of that city believed on him for the saying (logos) of the woman, which testified, He told me all that ever I did.
40 To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
So when the Samaritans were come unto him, they besought him that he would tarry with them: and he abode there two days.
41 Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
And many more believed because of his own word; (logos)
42 Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
And said unto the woman, Now we believe, not because of your saying: for we have heard him ourselves, and know that this is indeed the Christ, the Saviour of the world.
43 Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
Now after two days he departed thence, and went into Galilee.
44 (To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
For Jesus himself testified, that a prophet has no honour in his own country.
45 Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
Then when he was come into Galilee, the Galilaeans received him, having seen all the things that he did at Jerusalem at the feast: for they also went unto the feast.
46 Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
So Jesus came again into Cana of Galilee, where he made the water wine. And there was a certain nobleman, whose son was sick at Capernaum.
47 Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
When he heard that Jesus was come out of Judaea into Galilee, he went unto him, and besought him that he would come down, and heal his son: for he was at the point of death.
48 Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
Then said Jesus unto him, Except all of you see signs and wonders, all of you will not believe.
49 Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
The nobleman says unto him, Sir, come down before my child die.
50 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
Jesus says unto him, Go your way; your son lives. And the man believed the word (logos) that Jesus had spoken unto him, and he went his way.
51 Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
And as he was now going down, his servants met him, and told him, saying, Your son lives.
52 Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
Then enquired he of them the hour when he began to amend. And they said unto him, Yesterday at the seventh hour the fever left him.
53 Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
So the father knew that it was at the same hour, in the which Jesus said unto him, Your son lives: and himself believed, and his whole house.
54 Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.
This is again the second miracle that Jesus did, when he was come out of Judaea into Galilee.