< Yohanna 4 >
1 Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
When Jesus therefore understood that the Pharisees had heard that Jesus maketh more disciples, and baptizeth more than John,
2 ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
(Though Jesus himself did not baptize, but his disciples, )
3 Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
He left Judea, and went again into Galilee.
4 To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
And he was of necessity to pass through Samaria.
5 Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
He cometh therefore to a city of Samaria, which is called Sichar, near the land which Jacob gave to his son Joseph.
6 Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
Now Jacob’s well was there. Jesus therefore being wearied with his journey, sat thus on the well. It was about the sixth hour.
7 Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
There cometh a woman of Samaria, to draw water. Jesus saith to her: Give me to drink.
8 (Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
For his disciples were gone into the city to buy meats.
9 Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
Then that Samaritan woman saith to him: How dost thou, being a Jew, ask of me to drink, who am a Samaritan woman? For the Jews do not communicate with the Samaritans.
10 Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
Jesus answered, and said to her: If thou didst know the gift of God, and who he is that saith to thee, Give me to drink; thou perhaps wouldst have asked of him, and he would have given thee living water.
11 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
The woman saith to him: Sir, thou hast nothing wherein to draw, and the well is deep; from whence then hast thou living water?
12 Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
Art thou greater than our father Jacob, who gave us the well, and drank thereof himself, and his children, and his cattle?
13 Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
Jesus answered, and said to her: Whosoever drinketh of this water, shall thirst again;
14 amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn , aiōnios )
but he that shall drink of the water that I will give him, shall not thirst for ever: But the water that I will give him, shall become in him a fountain of water, springing up into life everlasting. (aiōn , aiōnios )
15 Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
The woman saith to him: Sir, give me this water, that I may not thirst, nor come hither to draw.
16 Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
Jesus saith to her: Go, call thy husband, and come hither.
17 Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
The woman answered, and said: I have no husband. Jesus said to her: Thou hast said well, I have no husband:
18 Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
For thou hast had five husbands: and he whom thou now hast, is not thy husband. This thou hast said truly.
19 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
The woman saith to him: Sir, I perceive that thou art a prophet.
20 Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
Our fathers adored on this mountain, and you say, that at Jerusalem is the place where men must adore.
21 Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
Jesus saith to her: Woman, believe me, that the hour cometh, when you shall neither on this mountain, not in Jerusalem, adore the Father.
22 Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
You adore that which you know not: we adore that which we know; for salvation is of the Jews.
23 Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
But the hour cometh, and now is, when the true adorers shall adore the Father in spirit and in truth. For the Father also seeketh such to adore him.
24 Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
God is a spirit; and they that adore him, must adore him in spirit and in truth.
25 Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
The woman saith to him: I know that the Messias cometh (who is called Christ). Therefore, when he is come, he will tell us all things.
26 Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
Jesus saith to her: I am he, who am speaking with thee.
27 Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
And immediately his disciples came; and they wondered that he talked with the woman. Yet no man said: What seekest thou? or, why talkest thou with her?
28 Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
The woman therefore left her waterpot, and went her way into the city, and saith to the men there:
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
Come, and see a man who has told me all things whatsoever I have done. Is not he the Christ?
30 Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
They went therefore out of the city, and came unto him.
31 Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
In the mean time the disciples prayed him, saying: Rabbi, eat.
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
But he said to them: I have meat to eat, which you know not.
33 Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
The disciples therefore said one to another: Hath any man brought him to eat?
34 Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
Jesus saith to them: My meat is to do the will of him that sent me, that I may perfect his work.
35 Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
Do you not say, There are yet four months, and then the harvest cometh? Behold, I say to you, lift up your eyes, and see the countries; for they are white already to harvest.
36 Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios )
And he that reapeth receiveth wages, and gathereth fruit unto life everlasting: that both he that soweth, and he that reapeth, may rejoice together. (aiōnios )
37 Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
For in this is the saying true: That it is one man that soweth, and it is another that reapeth.
38 Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
I have sent you to reap that in which you did not labour: others have laboured, and you have entered into their labours.
39 Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
Now of that city many of the Samaritans believed in him, for the word of the woman giving testimony: He told me all things whatsoever I have done.
40 To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
So when the Samaritans were come to him, they desired that he would tarry there. And he abode there two days.
41 Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
And many more believed in him because of his own word.
42 Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
And they said to the woman: We now believe, not for thy saying: for we ourselves have heard him, and know that this is indeed the Saviour of the world.
43 Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
Now after two days, he departed thence, and went into Galilee.
44 (To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
For Jesus himself gave testimony that a prophet hath no honour in his own country.
45 Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
And when he was come into Galilee, the Galileans received him, having seen all the things he had done at Jerusalem on the festival day; for they also went to the festival day.
46 Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
He came again therefore into Cana of Galilee, where he made the water wine. And there was a certain ruler, whose son was sick at Capharnaum.
47 Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
He having heard that Jesus was come from Judea into Galilee, went to him, and prayed him to come down, and heal his son; for he was at the point of death.
48 Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
Jesus therefore said to him: Unless you see signs and wonders, you believe not.
49 Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
The ruler saith to him: Lord, come down before that my son die.
50 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
Jesus saith to him: Go thy way; thy son liveth. The man believed the word which Jesus said to him, and went his way.
51 Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
And as he was going down, his servants met him; and they brought word, saying, that his son lived.
52 Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
He asked therefore of them the hour wherein he grew better. And they said to him: Yesterday, at the seventh hour, the fever left him.
53 Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
The father therefore knew, that it was at the same hour that Jesus said to him, Thy son liveth; and himself believed, and his whole house.
54 Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.
This is again the second miracle that Jesus did, when he was come out of Judea into Galilee.