< Yohanna 4 >
1 Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
When, therefore, the Lord knew that the Pharisees had heard that Jesus was making and immersing more disciples than John,
2 ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
(though not Jesus himself, but his disciples immersed, )
3 Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
he left Judea, and went again into Galilee.
4 To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
And it was necessary that he should go through Samaria.
5 Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
He came, therefore, to a city of Samaria, called Sychar, near the field that Jacob gave to his son Joseph.
6 Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
And Jacob’s well was there. Jesus, therefore, wearied with his journey, sat thus on the well. It was about the sixth hour.
7 Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
There came a woman of Samaria to draw water. And Jesus said to her: Give me to drink.
8 (Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
For his disciples had gone into the city to buy food.
9 Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
Then the woman of Samaria said to him: How is it that you, who are a Jew, ask drink of me, who am a woman of Samaria? (For the Jews have no social intercourse with the Samaritans.)
10 Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
Jesus answered and said to her: If you had known the gift of God, and who it is that said to you, Give me to drink, you would have asked of him, and he would have given you living water.
11 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
The woman said to him: Sir, you have no vessel with which you can draw, and the well is deep; whence have you that living water?
12 Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
Are you greater than our father Jacob, who gave us the well, and drank from it himself, and his sons, and his cattle?
13 Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
Jesus answered and said to her: Whoever drinks of this water, will thirst again;
14 amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn , aiōnios )
but whoever drinks of the water that I will give him, shall never thirst. But the water that I will give him, shall be in him a fountain of water springing up in order to eternal life. (aiōn , aiōnios )
15 Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
The woman said to him: Sir, give me this water, that I may not thirst, nor come hither to draw.
16 Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
Jesus said to her: Go, call your husband, and come hither.
17 Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
The woman answered and said: I have no husband. Jesus said to her: You have well said. I have no husband;
18 Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
for you have had five husbands, and he whom you now have is not your husband. In this you have spoken truly.
19 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
The woman said to him: Sir, I perceive that thou art a prophet.
20 Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
Our fathers worshiped in this mountain, and you Jews say that in Jerusalem is the place where we ought to worship.
21 Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
Jesus said to her: Woman, believe me, the hour is coming, when neither in this mountain, nor in Jerusalem, will you worship the Father.
22 Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
You worship you know not what; we know what we worship; for salvation is of the Jews.
23 Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
But the hour is coming, and now is, when the true worshipers will worship the Father in spirit and in truth; for the Father seeks such to worship him.
24 Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
God is spirit; and they that worship him, must worship him in spirit and in truth.
25 Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
The woman said to him: I know that Messiah (who is called Christ) is coming; when he comes, he will tell us all things.
26 Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
Jesus said to her: I who speak to you am he.
27 Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
And upon this his disciples came, and were astonished that he was talking with the woman. Yet no one said: What seekest thou? or, why talkest thou with her?
28 Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
Then the woman left her water-pot, and went into the city, and said to the men:
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
Come, see a man who has told me all things that I ever did. Is not this the Christ?
30 Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
Then they went out of the city and came to him.
31 Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
In the mean time, the disciples besought him, saying: Rabbi, eat.
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
But he said to them: I have food to eat of which you know not.
33 Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
Then the disciples said one to another: Has any one brought him food?
34 Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
Jesus said to them: My food is to do the will of him that sent me, and to finish his work.
35 Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
Do you not say, There are yet four months, and harvest comes? Behold, I say to you, Lift up your eyes, and look on the fields, for they are already white for the harvest.
36 Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios )
And he that reaps receives wages, and gathers fruit for life eternal; that he that sows, and he that reaps, may rejoice together. (aiōnios )
37 Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
For in this is the saying true, One sows and another reaps.
38 Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
I have sent you to reap that on which you bestowed no labor. Others have labored, and you have entered into their labors.
39 Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
And many of the Samaritans of that city believed on him, because of the word of the woman who testified, He told me all things that I ever did.
40 To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
When, therefore, the Samaritans came to him, they besought him to abide with them. And he abode there two days.
41 Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
And many more believed because of his own word;
42 Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
and they said to the woman: We no longer believe because of what you said, for we ourselves have heard, and we know that this is in truth the Savior of the world, the Christ.
43 Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
And after two days he departed thence, and went into Galilee;
44 (To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
for Jesus himself testified that a prophet has no honor in his own country.
45 Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
Therefore, when he came into Galilee, the Galileans received him, because they had seen all things that he had done in Jerusalem during the feast; for they themselves had gone to the feast.
46 Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
Then Jesus came again into Cana of Galilee, where he had made the water wine. And there was a certain courtier, whose sou was sick in Capernaum.
47 Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
When he heard that Jesus had come from Judea into Galilee, he went to him, and besought him that he would come down, and restore his son to health, for he was about to die.
48 Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
Then said Jesus to him: Unless you see signs and wonders, you will not believe.
49 Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
The courtier said to him: Sir, come down before my child die.
50 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
Jesus said to him: Go, your child lives. And the man believed the word that Jesus spoke, and departed.
51 Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
And as he was going down, his servants met him, and said: Your son lives.
52 Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
Then he inquired of them the hour in which he was restored to health. And they said to him: Yesterday, at the seventh hour, the fever left him.
53 Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
Then his father knew that it was in the same hour in which Jesus said to him, Your son lives. And he himself, and all his house, believed.
54 Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.
This is the second sign which Jesus did, when he came out of Judea into Galilee.