< Yohanna 4 >
1 Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
Da Herren nu erfarede, at Farisæerne havde hørt, at Jesus vandt flere Disciple og døbte flere end Johannes
2 ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
(skønt Jesus ikke døbte selv, men hans Disciple):
3 Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
da forlod han Judæa og drog atter bort til Galilæa.
4 To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
Men han maatte rejse igennem Samaria.
5 Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
Han kommer da til en By i Samaria, som kaldes Sykar, nær ved det Stykke Land, som Jakob gav sin Søn Josef.
6 Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
Og der var Jakobs Brønd. Jesus satte sig da, træt af Rejsen, ned ved Brønden; det var ved den sjette Time.
7 Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
En samaritansk Kvinde kommer for at drage Vand op. Jesus siger til hende: „Giv mig noget at drikke!”
8 (Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
Hans Disciple vare nemlig gaaede bort til Byen for at købe Mad.
9 Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
Da siger den samaritanske Kvinde til ham: „Hvorledes kan dog du, som er en Jøde, bede mig, som er en samaritansk Kvinde, om noget at drikke?” Thi Jøder holde ikke Samkvem med Samaritaner.
10 Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
Jesus svarede og sagde til hende: „Dersom du kendte Guds Gave, og hvem det er, som siger til dig: Giv mig noget at drikke, da bad du ham, og han gav dig levende Vand.”
11 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
Kvinden siger til ham: „Herre! du har jo intet at drage op med, og Brønden er dyb; hvorfra har du da det levende Vand?
12 Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
Mon du er større end vor Fader Jakob, som har givet os Brønden, og han har selv drukket deraf og hans Børn og hans Kvæg?”
13 Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
Jesus svarede og sagde til hende: „Hver den, som drikker af dette Vand, skal tørste igen.
14 amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn , aiōnios )
Men den, som drikker af det Vand, som jeg giver ham, skal til evig Tid ikke tørste; men det Vand, som jeg giver ham, skal blive i ham en Kilde af Vand, som fremvælder til et evigt Liv.” (aiōn , aiōnios )
15 Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
Kvinden siger til ham: „Herre! giv mig dette Vand, for at jeg ikke skal tørste og ikke komme hid for at drage op.”
16 Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
Jesus siger til hende: „Gaa bort, kald paa din Mand, og kom hid!”
17 Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
Kvinden svarede og sagde: „Jeg har ingen Mand.” Jesus siger til hende: „Med Rette sagde du: Jeg har ingen Mand.
18 Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
Thi du har haft fem Mænd; og han, som du nu har, er ikke din Mand. Det har du sagt sandt.”
19 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
Kvinden siger til ham: „Herre! jeg ser, at du er en Profet.
20 Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
Vore Fædre have tilbedet paa dette Bjerg, og I sige, at i Jerusalem er Stedet, hvor man bør tilbede.”
21 Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
Jesus siger til hende: „Tro mig, Kvinde, at den Time kommer, da det hverken skal være paa dette Bjerg eller i Jerusalem, at I tilbede Faderen.
22 Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
I tilbede det, I ikke kende; vi tilbede det, vi kende; thi Frelsen kommer fra Jøderne.
23 Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
Men den Time kommer, ja, den er nu, da de sande Tilbedere skulle tilbede Faderen i Aand og Sandhed; thi det er saadanne Tilbedere, Faderen vil have.
24 Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
Gud er Aand, og de, som tilbede ham, bør tilbede i Aand og Sandhed.”
25 Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
Kvinden siger til ham: „Jeg ved, at Messias kommer (hvilket betyder Kristus); naar han kommer, skal han kundgøre os alle Ting.”
26 Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
Jesus siger til hende: „Det er mig, jeg, som taler med dig.”
27 Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
Og i det samme kom hans Disciple, og de undrede sig over, at han talte med en Kvinde; dog sagde ingen: „Hvad søger du?” eller: „Hvorfor taler du med hende?”
28 Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
Da lod Kvinden sin Vandkrukke staa og gik bort til Byen og siger til Menneskene der:
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
„Kommer og ser en Mand, som har sagt mig alt det, jeg har gjort; mon han skulde være Kristus?”
30 Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
De gik ud af Byen og kom gaaende til ham.
31 Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
Imidlertid bade Disciplene ham og sagde: „Rabbi, spis!”
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
Men han sagde til dem: „Jeg har Mad at spise, som I ikke kende.”
33 Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
Da sagde Disciplene til hverandre: „Mon nogen har bragt ham noget at spise?”
34 Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
Jesus siger til dem: „Min Mad er, at jeg gør hans Villie, som udsendte mig, og fuldbyrder hans Gerning.
35 Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
Sige I ikke: Der er endnu fire Maaneder, saa kommer Høsten? Se, jeg siger eder, opløfter eders Øjne og ser Markerne; de ere allerede hvide til Høsten.
36 Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios )
Den, som høster, faar Løn og samler Frugt til et evigt Liv, saa at de kunne glæde sig tilsammen, baade den, som saar, og den, som høster. (aiōnios )
37 Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
Thi her er det Ord sandt: En saar, og en anden høster.
38 Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
Jeg har udsendt eder at høste det, som I ikke have arbejdet paa; andre have arbejdet, og I ere gaaede ind i deres Arbejde.”
39 Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
Men mange af Samaritanerne fra den By troede paa ham paa Grund af Kvindens Ord, da hun vidnede: „Han har sagt mig alt det, jeg har gjort.”
40 To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
Da nu Samaritanerne kom til ham, bade de ham om at blive hos dem; og han blev der to Dage.
41 Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
Og mange flere troede for hans Ords Skyld.
42 Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
Og til Kvinden sagde de: „Vi tro nu ikke længer for din Tales Skyld; thi vi have selv hørt, og vi vide, at denne er sandelig Verdens Frelser.”
43 Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
Men efter de to Dage gik han derfra til Galilæa.
44 (To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
Thi Jesus vidnede selv, at en Profet ikke bliver æret i sit eget Fædreland.
45 Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
Da han nu kom til Galilæa, toge Galilæerne imod ham, fordi de havde set alt det, som han gjorde i Jerusalem paa Højtiden; thi ogsaa de vare komne til Højtiden.
46 Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
Han kom da atter til Kana i Galilæa, hvor han havde gjort Vandet til Vin. Og der var en kongelig Embedsmand, hvis Søn laa syg i Kapernaum.
47 Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
Da denne hørte, at Jesus var kommen fra Judæa til Galilæa, gik han til ham og bad om, at han vilde komme ned og helbrede hans Søn; thi han var Døden nær.
48 Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
Da sagde Jesus til ham: „Dersom I ikke se Tegn og Undergerninger, ville I ikke tro.”
49 Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
Embedsmanden siger til ham: „Herre! kom, før mit Barn dør.”
50 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
Jesus siger til ham: „Gaa bort, din Søn lever.” Og Manden troede det Ord, som Jesus sagde til ham, og gik bort.
51 Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
Men allerede medens han var paa Hjemvejen, mødte hans Tjenere ham og meldte, at hans Barn levede.
52 Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
Da udspurgte han dem om den Time, i hvilken det var blevet bedre med ham; og de sagde til ham: „I Gaar ved den syvende Time forlod Feberen ham.”
53 Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
Da skønnede Faderen, at det var sket i den Time, da Jesus sagde til ham: „Din Søn lever;” og han troede selv og hele hans Hus.
54 Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.
Dette var det andet Tegn, som Jesus gjorde, da han var kommen fra Judæa til Galilæa.