< Yohanna 3 >

1 Akwai wani Bafarisiye mai suna Nikodimus, wani ɗan majalisar Yahudawa.
Now there was a man of the pharisees, whose name was Nicodemus, a ruler among the Jews:
2 Ya zo wurin Yesu da dad dare ya ce, “Rabbi, mun sani kai malami ne daga Allah. Gama ba wanda zai iya yin waɗannan abubuwan banmamaki da kake yi in Allah ba ya tare da shi.”
who came to Jesus by night, and said unto Him, Rabbi, we know that thou art a teacher come from God: for none can do these miracles which thou dost, unless God be with him.
3 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an sāke haihuwarsa.”
Jesus answered and said unto him, Verily verily I tell thee, Unless a man be born again, he cannot see the kingdom of God.
4 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya za a haifi mutum sa’ad da ya tsufa? Tabbatacce ba zai sāke koma sau na biyu a cikin mahaifiyarsa don a haife shi kuma ba!”
Nicodemus saith unto Him, How can a man be born when he is old? can he enter a second time into his mother's womb, and be born?
5 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an haife shi ta wurin ruwa da kuma Ruhu.
Jesus answered, I tell thee of a truth, Unless a man be born of water and of the Spirit, he cannot enter into the kingdom of God.
6 Jiki yakan haifi jiki, amma Ruhu yana haifi ruhu.
That, which is born of the flesh, is flesh; and that, which is born of the Spirit, is spirit.
7 Kada ka yi mamaki da na ce, ‘Dole ne a sāke haifarku.’
Do not wonder that I said unto thee, Ye must be born again.
8 Iska takan hura zuwa inda take so. Kai kakan ji motsinta, sai dai ba ka iya sanin inda take fitowa ko kuwa inda za ta. Haka yake ga duk wanda aka haifa ta wurin Ruhu.”
As the wind bloweth where it listeth, and thou hearest the sound of it, but knowest not whence it cometh, or whither it goeth; so is every one that is born of the Spirit.
9 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya wannan zai yiwu?”
Nicodemus answered and said unto Him, How can these things be?
10 Yesu ya ce, “Kai ma da kake malami na Isra’ila, ba ka fahimci waɗannan abubuwa ba?
Jesus answered and said unto him, Art thou a teacher of Israel and knowest not these things?
11 Gaskiya nake faɗa maka, muna magana a kan abin da muka sani, muka kuma shaida abin da muka gani ne, amma har yanzu kun ƙi ku karɓi shaidarmu.
I assure thee, that we speak what we know, and testify what we have seen; though ye receive not our testimony.
12 Na yi muku magana a kan abubuwan duniya amma ba ku gaskata ba; to, yaya za ku gaskata in na yi magana a kan abubuwan sama?
If I have told you earthly things and ye believe not, how will ye believe if I should tell you heavenly ones?
13 Ba wanda ya taɓa hawa zuwa sama sai wanda ya sauka daga sama, wato, Ɗan Mutum.
For no one hath ascended up into heaven, but He that came down from heaven, even the Son of man who is in heaven.
14 Kamar dai yadda Musa ya ɗaga maciji a hamada, haka dole ne a ɗaga Ɗan Mutum,
And as Moses lifted up the serpent in the wilderness, so must the Son of man be lifted up:
15 don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios g166)
that whosoever believeth on Him may not perish, but have eternal life. (aiōnios g166)
16 Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios g166)
For God so loved the world, that He gave his only begotten Son, that whosoever believeth on Him might not perish, but have everlasting life: (aiōnios g166)
17 Gama Allah bai aiki Ɗansa duniya don yă yi wa duniya hukunci ba, sai dai domin yă ceci duniya ta wurinsa.
for God sent not his son into the world to condemn the world, but that the world might be saved by Him.
18 Duk wanda ya gaskata da shi ba za a yi masa hukunci ba, amma duk wanda bai gaskata ba an riga an yi masa hukunci domin bai gaskata da sunan wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗan Allah ba.
He that believeth on Him is not condemned: but he that believeth not, is already condemned; because he hath not believed on the name of the only-begotten Son of God.
19 Hukuncin shi ne, Haske ya zo cikin duniya, amma mutane suka so duhu a maimakon haske domin ayyukansu mugaye ne.
And this is the condemnation, that light is come into the world, and men loved darkness rather than light, because their deeds were evil.
20 Duk mai aikata mugunta yana ƙin haske, ba zai kuwa zo cikin haske ba don yana tsoro kada ayyukansa su tonu.
For every one that doth evil, hateth the light; and he cometh not to the light, least his deeds should be reproved.
21 Amma duk mai rayuwa bisa ga gaskiya yakan zo cikin haske, domin a gani a sarari cewa ayyukan da ya yi an yi su ne ta wurin Allah.
But he that acts according to truth, cometh to the light, that his deeds may be made manifest, that they are wrought in God.
22 Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan Yahudiya, inda ya ɗan jima da su, ya kuma yi baftisma.
After these things came Jesus, and his disciples into the land of Judea: and He stayed with them there, and baptized.
23 To, Yohanna ma yana yin baftisma a Ainon kusa da Salim, saboda akwai ruwa da yawa a can, mutane kuwa suka yi ta zuwa don a yi musu baftisma.
And John also was baptizing in Enon near Salim; because there was much water there: and people came to him and were baptized.
24 (Wannan kuwa kafin a sa Yohanna a kurkuku.)
For John was not yet cast into prison.
25 Sai gardama ta tashi tsakanin waɗansu almajiran Yohanna da wani mutumin Yahuda a kan zancen al’adar tsarkakewa.
Now there arose a dispute between some of the disciples of John, and the Jews, about purifying.
26 Sai suka zo wurin Yohanna suka ce masa, “Rabbi, wancan mutumin da yake tare da kai a ƙetaren Urdun, wannan da ka ba da shaida a kansa sosai nan, yana baftisma, kuma kowa yana zuwa wurinsa.”
And they came to John, and said unto him, Rabbi, He that was with thee on the other side Jordan, to whom thou barest testimony, behold, He baptizeth and all the people come to Him.
27 Ga wannan zancen Yohanna ya amsa ya ce, “Mutum yakan karɓi kawai abin da aka ba shi ne daga sama.
John answered and said, A man can take nothing upon him, unless it be given him from heaven.
28 Ku kanku za ku shaida cewa na ce, ‘Ba ni ne Kiristi ba, sai dai an aiko ni ne in sha gabansa.’
Ye your selves bear me witness, that I said, I am not the Christ, but am sent before Him.
29 Ango ne mai amarya. Abokin da yake masa hidima yakan jira ya kuma saurara masa, yakan kuma cika da farin ciki sa’ad da ya ji muryar ango. Wannan farin cikin kuwa nawa ne, ya kuma cika a yanzu.
He that hath the bride is the bridegroom: but the friend of the bridegroom, who standeth and heareth him, rejoiceth with great joy at the bridegroom's voice. Therefore my joy is complete.
30 Dole ne yă yi ta ƙaruwa, ni kuma in yi ta raguwa.
He must increase, but I must decrease.
31 “Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa; wannan da ya zo daga ƙasa na ƙasa ne, yana kuma magana kamar wanda ya zo daga ƙasa ne. Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa.
He, that cometh from above, is above all: he that is of the earth, is earthly, and talketh like one of the earth:
32 Yana ba da shaidar abin da ya gani da kuma ya ji, duk da haka ba wanda ya yarda da shaidarsa.
but He that cometh from heaven, is above all: and what He hath seen and heard, this He testifieth: and yet scarce any one receiveth his testimony.
33 Mutumin da ya yarda da ita ya tabbatar da cewa Allah mai gaskiya ne.
He that hath received his testimony, hath set his seal to this, that God is true:
34 Gama wannan da Allah ya aiko yakan faɗi kalmomin Allah ne, gama Allah yana ba da Ruhu babu iyaka.
for He, whom God hath sent, speaketh the words of God: for God giveth the Spirit to Him not by measure.
35 Uban yana ƙaunar Ɗan ya kuma danƙa kome a hannuwansa.
The Father loveth the Son, and hath given all into his hand:
36 Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios g166)
wherefore he that believeth on the Son, hath eternal life; and he that obeyeth not the Son, shall not see life, but the wrath of God abideth on him. (aiōnios g166)

< Yohanna 3 >