< Yohanna 3 >

1 Akwai wani Bafarisiye mai suna Nikodimus, wani ɗan majalisar Yahudawa.
Now there was one of the Pharisees whose name was Nicodemus--a ruler among the Jews.
2 Ya zo wurin Yesu da dad dare ya ce, “Rabbi, mun sani kai malami ne daga Allah. Gama ba wanda zai iya yin waɗannan abubuwan banmamaki da kake yi in Allah ba ya tare da shi.”
He came to Jesus by night and said, "Rabbi, we know that you are a teacher from God; for no one can do these miracles which you are doing, unless God is with him.
3 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an sāke haihuwarsa.”
"In most solemn truth I tell you," answered Jesus, "that unless a man is born anew he cannot see the Kingdom of God."
4 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya za a haifi mutum sa’ad da ya tsufa? Tabbatacce ba zai sāke koma sau na biyu a cikin mahaifiyarsa don a haife shi kuma ba!”
"How is it possible," Nicodemus asked, "for a man to be born when he is old? Can he a second time enter his mother's womb and be born?"
5 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an haife shi ta wurin ruwa da kuma Ruhu.
"In most solemn truth I tell you," replied Jesus, "that unless a man is born of water and the Spirit, he cannot enter the Kingdom of God.
6 Jiki yakan haifi jiki, amma Ruhu yana haifi ruhu.
Whatever has been born of the flesh is flesh, and whatever has been born of the Spirit is spirit.
7 Kada ka yi mamaki da na ce, ‘Dole ne a sāke haifarku.’
Do not be astonished at my telling you, 'You must all be born anew.'
8 Iska takan hura zuwa inda take so. Kai kakan ji motsinta, sai dai ba ka iya sanin inda take fitowa ko kuwa inda za ta. Haka yake ga duk wanda aka haifa ta wurin Ruhu.”
The wind blows where it chooses, and you hear its sound, but you do not know where it comes from or where it is going. So is it with every one who has been born of the Spirit."
9 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya wannan zai yiwu?”
"How is all this possible?" asked Nicodemus.
10 Yesu ya ce, “Kai ma da kake malami na Isra’ila, ba ka fahimci waɗannan abubuwa ba?
"Are you," replied Jesus, "'the Teacher of Israel,' and yet do you not understand these things?
11 Gaskiya nake faɗa maka, muna magana a kan abin da muka sani, muka kuma shaida abin da muka gani ne, amma har yanzu kun ƙi ku karɓi shaidarmu.
In most solemn truth I tell you that we speak what we know, and give testimony of that of which we were eye-witnesses, and yet you all reject our testimony.
12 Na yi muku magana a kan abubuwan duniya amma ba ku gaskata ba; to, yaya za ku gaskata in na yi magana a kan abubuwan sama?
If I have told you earthly things and none of you believe me, how will you believe me if I tell you of things in Heaven?
13 Ba wanda ya taɓa hawa zuwa sama sai wanda ya sauka daga sama, wato, Ɗan Mutum.
There is no one who has gone up to Heaven, but there is One who has come down from Heaven, namely the Son of Man whose home is in Heaven.
14 Kamar dai yadda Musa ya ɗaga maciji a hamada, haka dole ne a ɗaga Ɗan Mutum,
And just as Moses lifted high the serpent in the Desert, so must the Son of Man be lifted up,
15 don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios g166)
in order that every one who trusts in Him may have the Life of the Ages." (aiōnios g166)
16 Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios g166)
For so greatly did God love the world that He gave His only Son, that every one who trusts in Him may not perish but may have the Life of Ages. (aiōnios g166)
17 Gama Allah bai aiki Ɗansa duniya don yă yi wa duniya hukunci ba, sai dai domin yă ceci duniya ta wurinsa.
For God did not send His Son into the world to judge the world, but that the world might be saved through Him.
18 Duk wanda ya gaskata da shi ba za a yi masa hukunci ba, amma duk wanda bai gaskata ba an riga an yi masa hukunci domin bai gaskata da sunan wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗan Allah ba.
He who trusts in Him does not come up for judgement. He who does not trust has already received sentence, because he has not his trust resting on the name of God's only Son.
19 Hukuncin shi ne, Haske ya zo cikin duniya, amma mutane suka so duhu a maimakon haske domin ayyukansu mugaye ne.
And this is the test by which men are judged--the Light has come into the world, and men loved the darkness more than they loved the Light, because their deeds were wicked.
20 Duk mai aikata mugunta yana ƙin haske, ba zai kuwa zo cikin haske ba don yana tsoro kada ayyukansa su tonu.
For every wrongdoer hates the light, and does not come to the light, for fear his actions should be exposed and condemned.
21 Amma duk mai rayuwa bisa ga gaskiya yakan zo cikin haske, domin a gani a sarari cewa ayyukan da ya yi an yi su ne ta wurin Allah.
But he who does what is honest and right comes to the light, in order that his actions may be plainly shown to have been done in God.
22 Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan Yahudiya, inda ya ɗan jima da su, ya kuma yi baftisma.
After this Jesus and His disciples went into Judaea; and there He made a stay in company with them and baptized.
23 To, Yohanna ma yana yin baftisma a Ainon kusa da Salim, saboda akwai ruwa da yawa a can, mutane kuwa suka yi ta zuwa don a yi musu baftisma.
And John too was baptizing at Aenon, near Salim, because there were many pools of water there; and people came and received baptism.
24 (Wannan kuwa kafin a sa Yohanna a kurkuku.)
(For John was not yet in prison.)
25 Sai gardama ta tashi tsakanin waɗansu almajiran Yohanna da wani mutumin Yahuda a kan zancen al’adar tsarkakewa.
As the result, a discussion having arisen on the part of John's disciples with a Jew about purification,
26 Sai suka zo wurin Yohanna suka ce masa, “Rabbi, wancan mutumin da yake tare da kai a ƙetaren Urdun, wannan da ka ba da shaida a kansa sosai nan, yana baftisma, kuma kowa yana zuwa wurinsa.”
they came to John and reported to him, "Rabbi, he who was with you on the other side of the Jordan and to whom you bore testimony is now baptizing, and great numbers of people are resorting to him."
27 Ga wannan zancen Yohanna ya amsa ya ce, “Mutum yakan karɓi kawai abin da aka ba shi ne daga sama.
"A man cannot obtain anything," replied John, "unless it has been granted to him from Heaven.
28 Ku kanku za ku shaida cewa na ce, ‘Ba ni ne Kiristi ba, sai dai an aiko ni ne in sha gabansa.’
You yourselves can bear witness to my having said, 'I am not the Christ,' but 'I am His appointed forerunner.'
29 Ango ne mai amarya. Abokin da yake masa hidima yakan jira ya kuma saurara masa, yakan kuma cika da farin ciki sa’ad da ya ji muryar ango. Wannan farin cikin kuwa nawa ne, ya kuma cika a yanzu.
He who has the bride is the bridegroom; and the bridegroom's friend who stands by his side and listens to him, rejoices heartily on account of the bridegroom's happiness. Therefore this joy of mine is now complete.
30 Dole ne yă yi ta ƙaruwa, ni kuma in yi ta raguwa.
He must grow greater, but I must grow less.
31 “Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa; wannan da ya zo daga ƙasa na ƙasa ne, yana kuma magana kamar wanda ya zo daga ƙasa ne. Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa.
He who comes from above is above all. He whose origin is from the earth is not only himself from the earth, his teaching also is from the earth. He who comes from Heaven is above all.
32 Yana ba da shaidar abin da ya gani da kuma ya ji, duk da haka ba wanda ya yarda da shaidarsa.
What He has seen and heard, to that He bears witness; but His testimony no one receives.
33 Mutumin da ya yarda da ita ya tabbatar da cewa Allah mai gaskiya ne.
Any man who has received His testimony has solemnly declared that God is true.
34 Gama wannan da Allah ya aiko yakan faɗi kalmomin Allah ne, gama Allah yana ba da Ruhu babu iyaka.
For He whom God has sent speaks God's words; for God does not give the Spirit with limitations."
35 Uban yana ƙaunar Ɗan ya kuma danƙa kome a hannuwansa.
The Father loves the Son and has entrusted everything to His hands.
36 Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios g166)
He who believes in the Son has the Life of the Ages; he who disobeys the Son will not enter into Life, but God's anger remains upon him. (aiōnios g166)

< Yohanna 3 >