< Yohanna 3 >

1 Akwai wani Bafarisiye mai suna Nikodimus, wani ɗan majalisar Yahudawa.
And there was a man of the Pharisees, named Nicodemus, a ruler of the Jews.
2 Ya zo wurin Yesu da dad dare ya ce, “Rabbi, mun sani kai malami ne daga Allah. Gama ba wanda zai iya yin waɗannan abubuwan banmamaki da kake yi in Allah ba ya tare da shi.”
This man came to him by night, and said to him, Rabbi, we know that thou hast come as a teacher from God; for no one can do these signs which thou doest, unless God be with him.
3 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an sāke haihuwarsa.”
Jesus answered and said to him, Truly, truly do I say to thee, Unless a man be born again, he cannot see the kingdom of God.
4 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya za a haifi mutum sa’ad da ya tsufa? Tabbatacce ba zai sāke koma sau na biyu a cikin mahaifiyarsa don a haife shi kuma ba!”
Nicodemus saith to him, How can a man be born when he is old? Can he enter his mother's womb a second time, and be born?
5 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an haife shi ta wurin ruwa da kuma Ruhu.
Jesus answered, Truly, truly do I say to thee, Unless a man be born of water and of the Spirit, he cannot enter the kingdom of heaven.
6 Jiki yakan haifi jiki, amma Ruhu yana haifi ruhu.
That which is born of the flesh, is flesh; and that which is born of the Spirit, is spirit.
7 Kada ka yi mamaki da na ce, ‘Dole ne a sāke haifarku.’
Marvel not that I said to thee, Ye must be born again.
8 Iska takan hura zuwa inda take so. Kai kakan ji motsinta, sai dai ba ka iya sanin inda take fitowa ko kuwa inda za ta. Haka yake ga duk wanda aka haifa ta wurin Ruhu.”
The wind bloweth where it will; and thou hearest the sound thereof, but knowest not whence it cometh, and whither it goeth: so is every one that is born of the Spirit.
9 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya wannan zai yiwu?”
Nicodemus answered and said to him, How can these things be?
10 Yesu ya ce, “Kai ma da kake malami na Isra’ila, ba ka fahimci waɗannan abubuwa ba?
Jesus answered and said to him, Art thou the teacher of Israel, and understandest not these things?
11 Gaskiya nake faɗa maka, muna magana a kan abin da muka sani, muka kuma shaida abin da muka gani ne, amma har yanzu kun ƙi ku karɓi shaidarmu.
Truly, truly do I say to thee, We speak that which we know, and testify that which we have seen; and ye receive not our testimony.
12 Na yi muku magana a kan abubuwan duniya amma ba ku gaskata ba; to, yaya za ku gaskata in na yi magana a kan abubuwan sama?
If I have told you earthly things, and ye believe not, how will ye believe if I tell you heavenly things?
13 Ba wanda ya taɓa hawa zuwa sama sai wanda ya sauka daga sama, wato, Ɗan Mutum.
And no one hath ascended into heaven, but he who came down from heaven, even the Son of man.
14 Kamar dai yadda Musa ya ɗaga maciji a hamada, haka dole ne a ɗaga Ɗan Mutum,
And as Moses lifted up the serpent in the wilderness, so must the Son of man be lifted up
15 don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios g166)
that every one who believeth in him may have everlasting life. (aiōnios g166)
16 Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios g166)
For God so loved the world, that he gave the only begotten Son, that every one who believeth in him may not perish, but may have everlasting life. (aiōnios g166)
17 Gama Allah bai aiki Ɗansa duniya don yă yi wa duniya hukunci ba, sai dai domin yă ceci duniya ta wurinsa.
For God sent not the Son into the world to condemn the world, but that through him the world might be saved.
18 Duk wanda ya gaskata da shi ba za a yi masa hukunci ba, amma duk wanda bai gaskata ba an riga an yi masa hukunci domin bai gaskata da sunan wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗan Allah ba.
He that believeth in him is not condemned; he that believeth not hath already been condemned, because he hath not believed in the name of the only begotten Son of God.
19 Hukuncin shi ne, Haske ya zo cikin duniya, amma mutane suka so duhu a maimakon haske domin ayyukansu mugaye ne.
And this is the condemnation, that the light hath come into the world, and men loved the darkness rather than the light; for their deeds were evil.
20 Duk mai aikata mugunta yana ƙin haske, ba zai kuwa zo cikin haske ba don yana tsoro kada ayyukansa su tonu.
For every one that doeth evil hateth the light, and cometh not to the light, lest his deeds should be reproved.
21 Amma duk mai rayuwa bisa ga gaskiya yakan zo cikin haske, domin a gani a sarari cewa ayyukan da ya yi an yi su ne ta wurin Allah.
But he that doeth the truth cometh to the light, that his deeds may be made manifest, that they are wrought in God.
22 Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan Yahudiya, inda ya ɗan jima da su, ya kuma yi baftisma.
After these things Jesus and his disciples came into the land of Judaea; and there he remained with them, and baptized.
23 To, Yohanna ma yana yin baftisma a Ainon kusa da Salim, saboda akwai ruwa da yawa a can, mutane kuwa suka yi ta zuwa don a yi musu baftisma.
And John also was baptizing in AEnon, near Salim, because there was much water there; and they came, and were baptized.
24 (Wannan kuwa kafin a sa Yohanna a kurkuku.)
For John was not yet thrown into prison.
25 Sai gardama ta tashi tsakanin waɗansu almajiran Yohanna da wani mutumin Yahuda a kan zancen al’adar tsarkakewa.
Then there arose a question on the part of John's disciples with a Jew about purifying.
26 Sai suka zo wurin Yohanna suka ce masa, “Rabbi, wancan mutumin da yake tare da kai a ƙetaren Urdun, wannan da ka ba da shaida a kansa sosai nan, yana baftisma, kuma kowa yana zuwa wurinsa.”
And they came to John, and said to him, Rabbi, he who was with thee beyond the Jordan, to whom thou hast borne witness, behold, he baptizeth, and all men are going to him.
27 Ga wannan zancen Yohanna ya amsa ya ce, “Mutum yakan karɓi kawai abin da aka ba shi ne daga sama.
John answered and said, A man can receive nothing, unless it be given him from heaven.
28 Ku kanku za ku shaida cewa na ce, ‘Ba ni ne Kiristi ba, sai dai an aiko ni ne in sha gabansa.’
Ye yourselves bear me witness, that I said, I am not the Christ, but that I was sent before that man.
29 Ango ne mai amarya. Abokin da yake masa hidima yakan jira ya kuma saurara masa, yakan kuma cika da farin ciki sa’ad da ya ji muryar ango. Wannan farin cikin kuwa nawa ne, ya kuma cika a yanzu.
He that hath the bride is the bridegroom; but the friend of the bridegroom, who standeth and heareth him, rejoiceth greatly because of the bridegroom's voice. This my joy then hath become full.
30 Dole ne yă yi ta ƙaruwa, ni kuma in yi ta raguwa.
He must increase, but I must decrease.
31 “Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa; wannan da ya zo daga ƙasa na ƙasa ne, yana kuma magana kamar wanda ya zo daga ƙasa ne. Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa.
He that cometh from above is above all. He that is from the earth is earthly, and speaketh earthly things; he that cometh from heaven
32 Yana ba da shaidar abin da ya gani da kuma ya ji, duk da haka ba wanda ya yarda da shaidarsa.
testifieth what he hath seen and heard; and no one receiveth his testimony.
33 Mutumin da ya yarda da ita ya tabbatar da cewa Allah mai gaskiya ne.
He that hath received his testimony hath set his seal that God is true.
34 Gama wannan da Allah ya aiko yakan faɗi kalmomin Allah ne, gama Allah yana ba da Ruhu babu iyaka.
For he whom God sent speaketh the words of God; for he giveth not the Spirit by measure.
35 Uban yana ƙaunar Ɗan ya kuma danƙa kome a hannuwansa.
The Father loveth the Son, and hath given all things into his hand.
36 Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios g166)
He that believeth in the Son hath everlasting life; and he that disobeyeth the Son shall not see life, but the wrath of God abideth on him. (aiōnios g166)

< Yohanna 3 >