< Yohanna 3 >
1 Akwai wani Bafarisiye mai suna Nikodimus, wani ɗan majalisar Yahudawa.
Now there was a man of the Pharisees named Niqadimus, a ruler of the Jewish people.
2 Ya zo wurin Yesu da dad dare ya ce, “Rabbi, mun sani kai malami ne daga Allah. Gama ba wanda zai iya yin waɗannan abubuwan banmamaki da kake yi in Allah ba ya tare da shi.”
This man came to him at night, and said to him, "Rabbi, we know that you are a teacher come from God, for no one can do these signs that you do, unless God is with him."
3 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an sāke haihuwarsa.”
Yeshua answered him, "Truly, truly, I tell you, unless one is born again he cannot see the Kingdom of God."
4 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya za a haifi mutum sa’ad da ya tsufa? Tabbatacce ba zai sāke koma sau na biyu a cikin mahaifiyarsa don a haife shi kuma ba!”
Niqadimus said to him, "How can anyone be born when he is old? Can he enter a second time into his mother's womb, and be born?"
5 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an haife shi ta wurin ruwa da kuma Ruhu.
Yeshua answered, "Truly, truly, I tell you, unless one is born of water and Rukha he cannot enter into the Kingdom of God.
6 Jiki yakan haifi jiki, amma Ruhu yana haifi ruhu.
That which is born of the flesh is flesh. That which is born of the Rukha is spirit.
7 Kada ka yi mamaki da na ce, ‘Dole ne a sāke haifarku.’
Do not be surprised that I said to you, 'You must be born again.'
8 Iska takan hura zuwa inda take so. Kai kakan ji motsinta, sai dai ba ka iya sanin inda take fitowa ko kuwa inda za ta. Haka yake ga duk wanda aka haifa ta wurin Ruhu.”
The wind blows where it wants to, and you hear its sound, but do not know where it comes from and where it is going. So is everyone who is born of the Rukha."
9 Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya wannan zai yiwu?”
Niqadimus answered and said to him, "How can these things be?"
10 Yesu ya ce, “Kai ma da kake malami na Isra’ila, ba ka fahimci waɗannan abubuwa ba?
Yeshua answered him, "Are you the teacher of Israyel, and do not understand these things?
11 Gaskiya nake faɗa maka, muna magana a kan abin da muka sani, muka kuma shaida abin da muka gani ne, amma har yanzu kun ƙi ku karɓi shaidarmu.
Truly, truly, I tell you, we speak that which we know, and testify of that which we have seen, but you do not accept our testimony.
12 Na yi muku magana a kan abubuwan duniya amma ba ku gaskata ba; to, yaya za ku gaskata in na yi magana a kan abubuwan sama?
If I told you earthly things and you do not believe, how will you believe if I tell you heavenly things?
13 Ba wanda ya taɓa hawa zuwa sama sai wanda ya sauka daga sama, wato, Ɗan Mutum.
And no one has ascended into heaven, but he who descended out of heaven, the Son of Man, who is in heaven.
14 Kamar dai yadda Musa ya ɗaga maciji a hamada, haka dole ne a ɗaga Ɗan Mutum,
And as Mushe lifted up the serpent in the wilderness, even so must the Son of Man be lifted up,
15 don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios )
so that everyone who believes in him may have life without end. (aiōnios )
16 Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios )
For this is how God loved the world: he gave his only Son, so that everyone who believes in him will not perish but have life without end. (aiōnios )
17 Gama Allah bai aiki Ɗansa duniya don yă yi wa duniya hukunci ba, sai dai domin yă ceci duniya ta wurinsa.
For God did not send his Son into the world to judge the world, but that the world should be saved through him.
18 Duk wanda ya gaskata da shi ba za a yi masa hukunci ba, amma duk wanda bai gaskata ba an riga an yi masa hukunci domin bai gaskata da sunan wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗan Allah ba.
The one who believes in him is not judged, but the one who does not believe has been judged already, because he has not believed in the name of the only Son of God.
19 Hukuncin shi ne, Haske ya zo cikin duniya, amma mutane suka so duhu a maimakon haske domin ayyukansu mugaye ne.
This is the judgment, that the light has come into the world, and people loved the darkness rather than the light, because their works were evil.
20 Duk mai aikata mugunta yana ƙin haske, ba zai kuwa zo cikin haske ba don yana tsoro kada ayyukansa su tonu.
For everyone who does evil hates the light, and does not come to the light, so that his works will not be exposed.
21 Amma duk mai rayuwa bisa ga gaskiya yakan zo cikin haske, domin a gani a sarari cewa ayyukan da ya yi an yi su ne ta wurin Allah.
But the one who does the truth comes to the light, that his works may be revealed, that they have been done in God."
22 Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan Yahudiya, inda ya ɗan jima da su, ya kuma yi baftisma.
After these things, Yeshua came with his disciples into the land of Yehuda. He stayed there with them, and was baptizing.
23 To, Yohanna ma yana yin baftisma a Ainon kusa da Salim, saboda akwai ruwa da yawa a can, mutane kuwa suka yi ta zuwa don a yi musu baftisma.
Now Yukhanan also was baptizing in Ain-Yaun near Shalim, because there was much water there. They came, and were baptized.
24 (Wannan kuwa kafin a sa Yohanna a kurkuku.)
For Yukhanan was not yet thrown into prison.
25 Sai gardama ta tashi tsakanin waɗansu almajiran Yohanna da wani mutumin Yahuda a kan zancen al’adar tsarkakewa.
Now a dispute arose between Yukhanan's disciples with a Jew about purification.
26 Sai suka zo wurin Yohanna suka ce masa, “Rabbi, wancan mutumin da yake tare da kai a ƙetaren Urdun, wannan da ka ba da shaida a kansa sosai nan, yana baftisma, kuma kowa yana zuwa wurinsa.”
And they came to Yukhanan, and said to him, "Rabbi, he who was with you beyond the Yurdinan, to whom you have testified, look, he is baptizing, and everyone is coming to him."
27 Ga wannan zancen Yohanna ya amsa ya ce, “Mutum yakan karɓi kawai abin da aka ba shi ne daga sama.
Yukhanan answered, "No one can receive anything, unless it has been given to him from heaven.
28 Ku kanku za ku shaida cewa na ce, ‘Ba ni ne Kiristi ba, sai dai an aiko ni ne in sha gabansa.’
You yourselves bear me witness that I said, 'I am not the Meshikha,' but, 'I have been sent before him.'
29 Ango ne mai amarya. Abokin da yake masa hidima yakan jira ya kuma saurara masa, yakan kuma cika da farin ciki sa’ad da ya ji muryar ango. Wannan farin cikin kuwa nawa ne, ya kuma cika a yanzu.
He who has the bride is the bridegroom; but the friend of the bridegroom, who stands and hears him, rejoices greatly because of the bridegroom's voice. So this joy of mine is now complete.
30 Dole ne yă yi ta ƙaruwa, ni kuma in yi ta raguwa.
He must increase, but I must decrease.
31 “Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa; wannan da ya zo daga ƙasa na ƙasa ne, yana kuma magana kamar wanda ya zo daga ƙasa ne. Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa.
He who comes from above is above all. He who is from the earth belongs to the earth, and speaks of the earth. He who comes from heaven is above all.
32 Yana ba da shaidar abin da ya gani da kuma ya ji, duk da haka ba wanda ya yarda da shaidarsa.
What he has seen and heard, of that he testifies; and no one receives his witness.
33 Mutumin da ya yarda da ita ya tabbatar da cewa Allah mai gaskiya ne.
He who has received his witness has set his seal to this, that God is true.
34 Gama wannan da Allah ya aiko yakan faɗi kalmomin Allah ne, gama Allah yana ba da Ruhu babu iyaka.
For he whom God has sent speaks the words of God; for he does not give the Rukha by measure.
35 Uban yana ƙaunar Ɗan ya kuma danƙa kome a hannuwansa.
The Father loves the Son, and has given all things into his hand.
36 Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios )
Whoever believes in the Son has everlasting life, but whoever refuses to believe in the Son won't see life, but the wrath of God remains on him." (aiōnios )