< Yohanna 21 >
1 Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
Po tem se je Jezus zopet prikazal učencem na morji Tiberijadskem; prikazal se je pa tako-le;
2 Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
Bili so skupaj Simon Peter in Tomaž, ki se imenuje Dvojček, in Natanael iz Kane Galilejske, in Zebedejeva, in dva druga izmed učencev njegovih.
3 Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
Reče jim Simon Peter: Ribe grem lovit. Rekó mu: Tudi mi pojdemo s teboj. Ter izidejo in vstopijo precej v ladjo, in tisto noč niso nič vjeli.
4 Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
Ko je pa uže jutro napočilo, stal je Jezus na bregu: ali učenci niso vedeli, da je Jezus.
5 Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
In reče jim Jezus: Otroci! jeli imate kakošne jedí? Odgovoré mu: Ne.
6 Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
On jim pa reče: Vrzite mrežo na desno stran ladje, pa boste našli. Ter vržejo, in niso je več mogli vleči od množice rib.
7 Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
Tedaj reče učenec, ta, kterega je Jezus ljubil, Petru: Gospod je. Simon Peter pa, ko zasliši, da je Gospod, opaše si srajco, (bil je namreč nag, ) in skoči v morje.
8 Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
A drugi učenci pridejo na ladjo, (niso bili namreč daleč od zemlje, nego kakih dvesto komolcev, ) in vlekli so mrežo z ribami.
9 Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
Ko pa izstopijo na zemljo, ugledajo ogenj naložen in na njem ribo položeno, in kruh.
10 Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
Velí jim Jezus: Prinesite od rib, ktere ste sedaj vjeli.
11 Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
Simon Peter vstopi, in izvleče mrežo na zemljo, polno velikih rib sto in tri in petdeset; in da si ravno jih je toliko bilo, ni se mreža raztrgala.
12 Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
Velí jim Jezus: Pridite, obedujte! Nobeden pa od učencev si ni upal vprašati ga: Kdo si ti? vedoč, da je Gospod.
13 Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
In Jezus pride, in vzeme kruh, in dá jim, in ravno tako ribo.
14 Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
To se je uže v tretje prikazal Jezus učencem svojim, odkar je vstal od mrtvih.
15 Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
A ko so poobedovali, reče Jezus Simonu Petru: Simon Jonov, ljubiš li me bolj, nego té? Reče mu: Dà, Gospod! ti véš, da te ljubim. Reče mu: Pasi jagnjeta moja.
16 Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
Reče mu zopet drugoč: Simon Jonov, ali me ljubiš? Reče mu: Dà, Gospod! ti veš, da te ljubim. Veli mu: Pasi ovce moje.
17 Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
Reče mu v tretje: Simon Jonov, ali me ljubiš? Peter postane žalosten, da mu je v tretje rekel: Ali me ljubiš? in reče mu: Gospod! ti vse véš; ti znaš, da te ljubim. Veli mu Jezus: Pasi ovce moje.
18 Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
Resnično resnično ti pravim: Ko si bil mlajši, opasoval si se sam, in hodil si, kamor si hotel; kedar boš pa star, raztegnil boš roke svoje, in drugi te bo opasal, in odpeljal te bo, kamor ne boš hotel.
19 Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
To je pa povedal, da je na znanje dal, s kakošno smrtjo bo oslavil Boga. In ko je to povedal, reče mu: Pojdi za menoj!
20 Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
Obrnivši se pa Peter, ugleda učenca, kterega je Jezus ljubil, da gre za njim, kteri je bil na večerji tudi legel na prsi njegove, in je bil rekel: Gospod! kdo je tisti, ki te bo izdal?
21 Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
Ko tega Peter ugleda, reče Jezusu: Gospod! Kaj pa ta?
22 Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
Reče mu Jezus: Če hočem, da ostane dotlej, ko pridem, kaj tebi za to? Ti pojdi za menoj.
23 Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
In razglasila se je med brati ta beseda: Ta učenec ne bo umrl. Ali Jezus mu ni bil rekel, da ne bo umrl; nego: Če hočem, da ostane dotlej, ko pridem, kaj tebi za to?
24 Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
Ta učenec je ta, ki pričuje za to, in je napisal to; in vémo, da je pričevanje njegovo resnično.
25 Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.
Je pa še drugega veliko, kar je storil Jezus, in to, ko bi se posamez vse napisalo, menim, da tudi ves svet ne bi imel prostora za bukve, ktere bi se napisale. Amen.