< Yohanna 21 >
1 Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
Emva kwalezizinto uJesu wabuya wazibonakalisa kubafundi elwandle lweTiberiyasi; njalo wazibonakalisa ngalindlela.
2 Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
Babendawonye oSimoni Petro, loTomasi othiwa nguDidimusi, loNathaniyeli oweKana yeGalili, lamadodana kaZebediya, labanye ababili babafundi bakhe.
3 Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
USimoni Petro wathi kubo: Ngiyagola inhlanzi. Bathi kuye: Lathi sizahamba lawe. Basebephuma bahle bangena emkhunjini, kodwa ngalobobusuku kababambanga lutho.
4 Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
Kwathi sekusemadabukakusa uJesu wema ekhunjini; kodwa abafundi babengazi ukuthi nguJesu.
5 Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
Ngakho uJesu wathi kubo: Bantwana, lilokudla yini? Bamphendula bathi: Hatshi.
6 Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
Wasesithi kubo: Phosani imbule ehlangothini lokunene lomkhumbi, njalo lizathola. Basebephosa, njalo babengaselakho ukulidonsa ngenxa yobunengi benhlanzi.
7 Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
Ngakho lowomfundi uJesu ayemthanda wathi kuPetro: YiNkosi. USimoni Petro, esezwile ukuthi yiNkosi, wagqoka isembatho (ngoba wayenqunu), waseziphosela olwandle.
8 Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
Kodwa abanye abafundi beza ngomkolo, bedonsa imbule lenhlanzi, ngoba babengekhatshana lomhlabathi, kodwa kungaba zingalo ezingamakhulu amabili.
9 Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
Kwathi sebekhuphukele emhlabathini, babona umlilo wamalahle khona, lenhlanzi zibekwe phezu kwawo, lesinkwa.
10 Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
UJesu wathi kubo: Lethani ezinye zezinhlanzi elisanda kuzibamba.
11 Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
USimoni Petro wasekhwela, wahudulela imbule emhlabathini, ligcwele inhlanzi ezinkulu, ikhulu lamatshumi amahlanu lantathu; njalo lanxa zazinengi kangaka, imbule kalidabukanga.
12 Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
UJesu wathi kubo: Wozani lidle. Kodwa kakho kubafundi owaba lesibindi sokumbuza ukuthi: Ungubani wena? besazi ukuthi yiNkosi.
13 Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
UJesu wasesiza, wathatha isinkwa, wabanika, lenhlanzi ngokufananayo.
14 Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
Lokhu sekungokwesithathu uJesu ebonakaliswa kubafundi, esevukile kwabafileyo.
15 Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
Sebedlile, uJesu wathi kuSimoni Petro: Simoni kaJona, uyangithanda kulalaba yini? Wathi kuye: Yebo Nkosi; wena uyazi ukuthi ngiyakuthanda. Wathi kuye: Phana amawundlu ami ukudla.
16 Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
Wabuya wathi kuye ngokwesibili: Simoni kaJona, uyangithanda yini? Wathi kuye: Yebo Nkosi, wena uyazi ukuthi ngiyakuthanda. Wathi kuye: Yelusa izimvu zami.
17 Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
Wathi kuye ngokwesithathu: Simoni kaJona, uyangithanda yini? UPetro wadabuka ngoba wathi kuye ngokwesithathu: Uyangithanda yini? Wasesithi kuye: Nkosi, wena uyakwazi konke; wena uyakwazi ukuthi ngiyakuthanda. UJesu wathi kuye: Phana izimvu zami ukudla.
18 Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
Ngiqinisile, ngiqinisile, ngithi kuwe: Usemutsha, wawuzibhinca, uhamba lapho othanda khona; kodwa nxa usumdala, uzakwelula izandla zakho, omunye abesekubopha, akuse lapho ongathandi khona.
19 Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
Lalokhu wakutsho, etshengisa indlela yokufa ayezadumisa uNkulunkulu ngayo. Esetshilo lokhu wathi kuye: Ngilandela.
20 Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
UPetro etshibilika wabona umfundi uJesu amthandayo elandela, yena futhi owayeyeme esifubeni sakhe ekudleni kwantambama wathi: Nkosi, ngubani ozakunikela?
21 Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
Kwathi uPetro embona wathi kuJesu: Nkosi, lo-ke?
22 Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
UJesu wathi kuye: Uba ngithanda ukuthi ahlale ngize ngifike, ulani lakho? Ngilandela wena.
23 Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
Ngakho lelilizwi laphumela kubazalwane, ukuthi lowomfundi kayikufa; kanti uJesu katshongo kuye ukuthi kayikufa; kodwa wathi: Uba ngithanda ukuthi ahlale ngize ngifike, ulani lakho?
24 Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
Nguye lowomfundi ofakaza ngalezizinto, lozibhalileyo; njalo siyazi ukuthi ubufakazi bakhe buliqiniso.
25 Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.
Njalo zikhona lezinye izinto ezinengi uJesu azenzayo, uba bezilotshiwe zonke ngazinye, ngicabanga ukuthi lomhlaba lawo ubungebe lendawo yezingwalo ezilotshiweyo. Ameni.