< Yohanna 21 >
1 Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
Baada jha mambo aghu Yesu kwidhihirisha kabhele kwa bhanafunzi mu Bahari jha Tiberia; efe ndo kyaakidhihirishi muene:
2 Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
Simoni Petro ajhele pamonga ni Thomaso jhaakutibhweghe Didimas, Nathanaeli ghwa Kana jha Galilaya, bhana bha Zebedayo ni bhanafunzi bhangi bhabhele bha Yesu.
3 Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
Simoni Petro akabhajobhela, “Nene nilota kulobha somba.” Ni bhene bhakan'jobhela, “Tete, pia twilota pamonga ni bhebhe.” Bhakalota bhakajhingila mu mashua, lakini kinu kyoha eku bhakilepi khenu.
4 Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
Ni lukhela bho kubhalele, Yesu ajhemili kundema, na bhene bhanafunzi bhamanyilepi kujha ndo Yesu.
5 Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
Kisha Yesu akabhajobhela, “Bhasongolo, mujhe ni kyokyoha kya kulya?” Na bhene bakan'jibu, “Lepi.”
6 Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
Akabhajobhela, “Muselesiajhi nkwabhu lubhafu kwa kuume bhwa mashua, na mu mwibeta kukabha kiasi.” Kwa hiyo bhakaselesya nkwabhu ni bhene bhabhwesilepi kufuta kabhele kwandabha jha bhwingi bhwa somba.
7 Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
Basi mwanafunzi jhola ambajhe Yesu an'ganili akan'jobhela Petro, “Ndo Bwana.” Ni muene Simoni Petro bho apeliki kujha ndo Bwana, akakikonga liguanda lya muene (ndabha alifwali lepi kinofu), kisha akakisopa mu masi.
8 Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
Bhanafunzi bhangi bhala bhakahida mu mashua (kwani bhajhelepi patali ni pwani, kama mita mia moja kuhomela ufukweni), na bhene bhakajha bhifuta mikwabhu ghela ambaghyo ghyamemili somba.
9 Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
Bho bhafikili ufukweni, bhaghubhwene muoto ghwa mkaa pala ni panani pa muene kwajhele ni somba pamonga ni mkate.
10 Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
Yesu akabhajobhela, “Muletayi baadhi jha somba sya mulobhili henu naha.”
11 Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
Basi Simoni Petro akakuela ni kuukokota nkwabhu bhwa wamemili somba sibhaha, kiasi kya somba 153; japo bhajhebhingi, nkwabhu bhola bhwakachwiki lepi.
12 Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
Yesu akabhajobhela, “Muhidayi mkabhayi kifungua kinywa.” Ajhelepi hata mmonga ghwa bhanafunzi jhaan'kotili, “Bhebhe ghwa niani?” Bhamanyili kujha ajhele Bwana.
13 Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
Yesu akahida, akautola n'kate bhola, kisha akabhapela, akabhomba mebhu niku somba sela.
14 Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
Ejhe jha jhele mara jha tatu kwa Yesu kwidhihirisha kwa bhanafunzi bha muene baada jha kufufuka kuhoma kwa bhafu.
15 Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
Baada jha kufungula kinywa, Yesu akan'jobhela Simoni Petro, “Simoni mwana ghwa Yohana je, uniganili nene kuliko abha?” Petro akajibu, “Ena, Bwana; “Bhebhe umanyili kujha nene nikuganili.” Yesu akan'jobhela, “Lesyajhi bhanakondoo bha nene.”
16 Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
Akan'jobhela mara jha pili, “Simoni mwana ghwa Yona, je, uniganili?” Petro akan'jobhela, “Ena, Bwana; bhebhe umanyili kujha nikuganili. “Yesu akan'jobhela, “Dimayi kondoo bhangu.”
17 Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
Akan'jobhela kabhele mara jha tatu, “Simoni, mwana ghwa Yohana, Je uniganili?” Ni muene Petro ahuzuniki kwa vile kyaan'jobhili mara jha tatu, “Je Bhebhe uniganili?” Ni muene akan'jobhela, “Bwana, umanyili ghoha; umanyili kujha nikuganili.” Yesu akan'jobhela, Lesiajhi kondoo bha nene.
18 Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
Aminiayi, aminiayi, nikujobhela, bho ghwen'songolo ghwasobhelili kufwala nghobho muene ni kulota kokuoha khola kwa ulondeghe; lakini paghwibetakujha ghwe nseya, ghwibetakugholosya mabhoko gha jhobhi, ni jhongi ibetakufwalika nghobho ni kukupeleka kwa ulondeghe lepi kulota.”
19 Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
Yesu ajobhi agha ili kulasya ni aina jheleku jha kifo ambakyo Petro ngaan'tukuizi K'yara. Baada jha kujha ajobhili agha, akan'jobhela Petro, “Nikesiajhi.”
20 Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
Petro akageuka ni kumbona jhola mwanafunzi ambajhe Yesu an'ganili akabhakesya- Ojho ndo ajhele akijheghemisi mu kifua kya Yesu wakati wa kyakulya kya kimihi ni kun'kota, “Bwana, niani jhaibetakusaliti?”
21 Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
Petro ambwene ni kisha akan'kota Yesu, “Bwana, Ojho munu ibetakubhomba kiki?”
22 Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
Yesu akan'jibu, “Kama nilonda abakilayi mpaka pa nibetakuhida, e'lu likuhusu kiki?” Nikesiajhi.”
23 Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
Kwa hiyo habari ejhe jhikaenela miongoni mwa bhala ndugu, kwamba mwanafunzi ojhui ibetalepi kufwa. Lakini Yesu an'jobhilepi Petro kujha, mwanafunzi ojhu ifwa lepi, “Kama nilonda muene abakilayi mpaka pa nibetakuhida ghikuhusu kiki?”
24 Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
Ojho ndo mwanafunzi jhaibetakupisya ushuhuda bhwa mambo agha, na ndo jhaalembili mambo agha, na tumanyili jha kujha ushuhuda bhwa muene bhwa bhukweli.
25 Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.
Kuna mambo ghangi ambagho Yesu aghabhombili. Kama kila limonga ngalijhandikibhu, nidhanila kwamba ulimwengu bhuene ngabhutoshilepi kufibheka fitabu ambafyo ngafilembibhu.