< Yohanna 21 >

1 Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
Après ces choses, Jésus se manifesta encore aux disciples près de la mer de Tibérias; et il se manifesta ainsi:
2 Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
Simon Pierre, et Thomas, appelé Didyme, et Nathanaël de Cana de Galilée, et les [fils] de Zébédée, et deux autres de ses disciples étaient ensemble.
3 Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
Simon Pierre leur dit: Je m’en vais pêcher. Ils lui disent: Nous allons aussi avec toi. Ils sortirent, et montèrent dans le bateau: et cette nuit-là ils ne prirent rien.
4 Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
Et le matin venant déjà, Jésus se tint sur le rivage; les disciples toutefois ne savaient pas que c’était Jésus.
5 Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
Jésus donc leur dit: Enfants, avez-vous quelque chose à manger? Ils lui répondirent: Non.
6 Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
Et il leur dit: Jetez le filet au côté droit du bateau, et vous trouverez. Ils le jetèrent donc, et ils ne pouvaient plus le tirer, à cause de la multitude des poissons.
7 Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
Ce disciple donc que Jésus aimait, dit à Pierre: C’est le Seigneur. Simon Pierre donc, ayant entendu que c’était le Seigneur, ceignit sa robe de dessus, car il était nu, et se jeta dans la mer.
8 Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
Et les autres disciples vinrent dans le petit bateau (car ils n’étaient pas loin de terre, mais à environ 200 coudées), traînant le filet de poissons.
9 Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
Quand ils furent donc descendus à terre, ils voient là de la braise, et du poisson mis dessus, et du pain.
10 Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
Jésus leur dit: Apportez quelques-uns des poissons que vous venez de prendre.
11 Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
Simon Pierre monta, et tira le filet à terre, plein de 153 gros poissons; et quoiqu’il y en eût tant, le filet n’avait pas été déchiré.
12 Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
Jésus leur dit: Venez, dînez. Et aucun des disciples n’osait lui demander: Qui es-tu? sachant que c’était le Seigneur.
13 Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
Jésus vient et prend le pain, et le leur donne, et de même le poisson.
14 Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
Ce fut là la troisième fois déjà que Jésus fut manifesté aux disciples, après qu’il fut ressuscité d’entre les morts.
15 Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
Lors donc qu’ils eurent dîné, Jésus dit à Simon Pierre: Simon, [fils] de Jonas, m’aimes-tu plus que [ne font] ceux-ci? Il lui dit: Oui, Seigneur, tu sais que je t’aime. Il lui dit: Pais mes agneaux.
16 Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
Il lui dit encore une seconde fois: Simon, [fils] de Jonas, m’aimes-tu? Il lui dit: Oui, Seigneur, tu sais que je t’aime. Il lui dit: Sois berger de mes brebis.
17 Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
Il lui dit pour la troisième fois: Simon, [fils] de Jonas, m’aimes-tu? Pierre fut attristé de ce qu’il lui disait pour la troisième fois: M’aimes-tu? Et il lui dit: Seigneur, tu connais toutes choses, tu sais que je t’aime. Jésus lui dit: Pais mes brebis.
18 Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
En vérité, en vérité, je te dis: Quand tu étais jeune, tu te ceignais, et tu allais où tu voulais; mais quand tu seras devenu vieux, tu étendras les mains, et un autre te ceindra, et te conduira où tu ne veux pas.
19 Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
Or il dit cela pour indiquer de quelle mort il glorifierait Dieu. Et quand il eut dit cela, il lui dit: Suis-moi.
20 Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
Pierre, se retournant, voit suivre le disciple que Jésus aimait, qui aussi, durant le souper, s’était penché sur sa poitrine, et avait dit: Seigneur, lequel est celui qui te livrera?
21 Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
Pierre, le voyant, dit à Jésus: Seigneur, et celui-ci, – que [lui arrivera-t-il]?
22 Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
Jésus lui dit: Si je veux qu’il demeure jusqu’à ce que je vienne, que t’importe? Toi, suis-moi.
23 Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
Cette parole donc se répandit parmi les frères, que ce disciple-là ne mourrait pas. Et Jésus ne lui avait pas dit qu’il ne mourrait pas, mais: Si je veux qu’il demeure jusqu’à ce que je vienne, que t’importe?
24 Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
C’est ce disciple-là qui rend témoignage de ces choses, et qui a écrit ces choses, et nous savons que son témoignage est vrai.
25 Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.
Et il y a aussi plusieurs autres choses que Jésus a faites, lesquelles, si elles étaient écrites une à une, je ne pense pas que le monde même puisse contenir les livres qui seraient écrits.

< Yohanna 21 >