< Yohanna 21 >
1 Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
After these things, Iesus shewed himselfe againe to his disciples at the sea of Tiberias: and thus shewed he himselfe:
2 Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
There were together Simon Peter, and Thomas, which is called Didymus, and Nathanael of Cana in Galile, and the sonnes of Zebedeus, and two other of his disciples.
3 Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
Simon Peter said vnto them, I go a fishing. They said vnto him, We also will goe with thee. They went their way and entred into a ship straightway, and that night caught they nothing.
4 Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
But when the morning was nowe come, Iesus stoode on the shore: neuerthelesse the disciples knewe not that it was Iesus.
5 Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
Iesus then said vnto them, Syrs, haue ye any meate? They answered him, No.
6 Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
Then he said vnto them, Cast out the net on the right side of the ship, and ye shall finde. So they cast out, and they were not able at all to draw it, for the multitude of fishes.
7 Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
Therefore said the disciple whom Iesus loued, vnto Peter, It is the Lord. When Simon Peter heard that it was the Lord, he girded his coate to him (for he was naked) and cast himselfe into the sea.
8 Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
But the other disciples came by shippe (for they were not farre from land, but about two hundreth cubites) and they drewe the net with fishes.
9 Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
Assoone then as they were come to land, they sawe hoate coales, and fish laide thereon, and bread.
10 Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
Iesus saide vnto them, Bring of the fishes, which ye haue nowe caught.
11 Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
Simon Peter stepped foorth and drewe the net to land, full of great fishes, an hundreth, fiftie and three: and albeit there were so many, yet was not the net broken.
12 Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
Iesus saide vnto them, Come, and dine. And none of the disciples durst aske him, Who art thou? seeing they knewe that he was the Lord.
13 Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
Iesus then came and tooke bread, and gaue them, and fish likewise.
14 Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
This is now the third time that Iesus shewed himselfe to his disciples, after that he was risen againe from the dead.
15 Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
So when they had dined, Iesus said to Simon Peter, Simon the sonne of Iona, louest thou me more then these? He said vnto him, Yea Lord, thou knowest that I loue thee. He said vnto him, Feede my lambes.
16 Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
He said to him againe the second time, Simon the sonne of Iona, louest thou me? He said vnto him, Yea Lord, thou knowest that I loue thee. He said vnto him, Feede my sheepe.
17 Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
He said vnto him the third time, Simon the sonne of Iona, louest thou me? Peter was sorie because he said to him the third time, Louest thou me? and said vnto him, Lord, thou knowest all things: thou knowest that I loue thee. Iesus saide vnto him, Feede my sheepe.
18 Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
Verely, verely I say vnto thee, When thou wast yong, thou girdedst thy selfe, and walkedst whither thou wouldest: but when thou shalt be olde, thou shalt stretch foorth thine hands, and another shall gird thee, and lead thee whither thou wouldest not.
19 Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
And this spake he signifying by what death he shoulde glorifie God. And when he had said this, he said to him, Folowe me.
20 Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
Then Peter turned about, and sawe the disciple whom JESUS loued, folowing, which had also leaned on his breast at supper, and had saide, Lord, which is he that betrayeth thee?
21 Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
When Peter therefore sawe him, he saide to Iesus, Lord, what shall this man doe?
22 Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
Iesus said vnto him, If I will that he tarie till I come, what is it to thee? follow thou me.
23 Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
Then went this worde abroade among the brethren, that this disciple shoulde not die. Yet Iesus saide not to him, He shall not die: but if I will that he tarie till I come, what is it to thee?
24 Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
This is that disciple, which testifieth of these things, and wrote these things, and we know that his testimonie is true.
25 Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.
Nowe there are also many other things which Iesus did, the which if they should be written euery one, I suppose the world coulde not conteine the bookes that shoulde be written, Amen.