< Yohanna 21 >

1 Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
After this, Jesus showed himself again to his disciples, at the sea of Tiberias. And he showed himself in this way.
2 Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
There were together, Simon Peter, and Thomas called Didymus, and Nathaniel of Cana of Galilee, and the sons of Zebedee, and two others of his disciples.
3 Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
Simon Peter said to them: I am going a fishing. They said to him: We also are going with you. They went out and entered the ship; and that night they caught nothing.
4 Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
But when the morning had now come, Jesus stood on the shore; but the disciples knew not that it was Jesus.
5 Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
Then Jesus said to them: Children, have you any food? They answered him: No.
6 Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
He said to them: Throw the net on the right side of the ship, and you will find. They threw it, there fore, and were no longer able to draw it for the multitude of fishes.
7 Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
Then that disciple whom Jesus loved said to Peter: It is the Lord. And when Simon Peter heard that it was the Lord, he girded on his outer coat, for he had on his inner garment only, and threw himself into the sea.
8 Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
And the other disciples came in a little ship, dragging the net with fishes, for they were not far from the land, only about two hundred cubits.
9 Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
As soon as they had come to the land, they saw there a fire of coals, and fish lying upon it, and bread.
10 Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
Jesus said to them; Bring of the fish that you have just taken.
11 Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
Simon Peter went and drew the net to the land, full of large fishes, a hundred and fifty-three. And though they were so many, the net did not break.
12 Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
Jesus said to them: Come and breakfast. But no one of the disciples durst ask him, Who art thou? because they knew it was the Lord.
13 Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
Then Jesus came and took the bread, and gave it to them, and the fish likewise.
14 Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
This was now the third occasion on which Jesus showed himself to his disciples, after he had risen from the dead.
15 Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
When, therefore, they had taken breakfast, Jesus said to Simon Peter: Simon, son of Jonah, Do you love me more than these? He said to him: Yes, Lord, thou knowest that I love thee. He said to him: Feed my lambs.
16 Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
He said to him again a second time: Simon, son of Jonah, do you love me? He said to him: Yes, Lord, thou knowest that I love thee. He said to him: Be a shepherd to my sheep.
17 Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
He said to him a third time: Simon, son of Jonah, do you love me? Peter was grieved because he said to him the third time, Do you love me? And he said to him: Lord, thou knowest all things, thou knowest that I love thee. Jesus said to him: Feed my sheep.
18 Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
Verily, verily I say to you, when you were young, you girded yourself, and walked whither you chose; but when you have become old, you shall stretch forth your hands, and another shall gird you, and lead you whither you would not.
19 Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
But this he said, signifying by what death he would glorify God. And when he had spoken this, he said to him: Follow me.
20 Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
Then Peter, turning about, saw the disciple that Jesus loved, following, who also reclined at supper upon his breast, and said: Lord, who is he that delivers thee up?
21 Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
Peter seeing this one, said to Jesus: Lord, what shall this one do?
22 Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
Jesus said to him: If I will that he remain till I come, what is that to you? Do you follow me.
23 Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
Therefore, this saying went out among the brethren, that that disciple should not die. Yet Jesus did not say to him, He shall not die; but, If I will that he remain till I come, what is that to you?
24 Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
This is the disciple who testifies of these things, and who has written these things; and we know that his testimony is true.
25 Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.
And there are also many other things that Jesus did; if they should be written, every one of them, I suppose that not even the world itself could contain the books that would be written.

< Yohanna 21 >