< Yohanna 20 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, tun da sauran duhu, Maryamu Magdalin ta tafi kabarin ta kuwa tarar an kawar da dutsen daga bakin kabarin.
Now on the first day of the week Mary Magdalene cometh early in the morning, while it was yet dark, to the sepulchre, and seeth the stone taken away from the sepulchre.
2 Sai ta zo da gudu wajen Siman Bitrus da ɗayan almajirin, wanda Yesu yake ƙauna, ta ce, “Sun ɗauke Ubangiji daga kabarin, ba mu kuma san inda suka sa shi ba!”
She therefore runneth and cometh to Simon Peter, and to the other disciple whom Jesus loved, and saith unto them, They have taken away the Lord out of the sepulchre, and we know not where they have laid Him.
3 Sai Bitrus da almajirin nan suka nufi kabarin.
Peter therefore went out, and that other disciple, and came to the sepulchre.
4 Dukansu biyu suna gudu, amma ɗayan almajirin ya tsere wa Bitrus ya kuma fara kai kabarin.
So they both ran together, but the other disciple out-ran Peter, and came first to the sepulchre:
5 Ya sunkuya ya duba ciki ya ga ƙyallayen lilin ne kwance a can amma bai shiga ba.
and stooping down to look in saw the linen cloths lying; but did not go in.
6 Sa’an nan Siman Bitrus, wanda yake bayansa, ya iso ya kuwa wuce cikin kabarin. Ya ga ƙyallayen lilin kwance a can,
Then cometh Simon Peter, who followed him, and went into the sepulchre, and seeth the linen cloths lying there;
7 haka ma zanen binnewar da aka naɗe kan Yesu da shi. Zanen a naɗe yake shi kaɗai, a keɓe da lilin ɗin.
and the napkin that was upon his head, not laid with the linen cloths, but folded up by itself.
8 A ƙarshe sai almajirin nan, wanda ya kai kabarin da farko, shi ma ya shiga. Ya gani ya kuma gaskata.
Then went in also the other disciple; who came first to the sepulchre, and he saw and believed.
9 (Har yanzu ba su fahimci Nassin nan da ya ce lalle ne Yesu yă tashi daga matattu ba.)
For they did not before understand the scripture, that He must rise from the dead.
10 Sai almajiran suka koma zuwa inda suke zama.
So the two disciples went away again to their own company.
11 Maryamu kuwa ta tsaya a bakin kabarin daga waje tana kuka. Da tana cikin kuka, sai ta sunkuya ta leƙa cikin kabarin,
But Mary stood without near the sepulchre weeping: and as she wept she stooped down to look into the sepulchre; and there seeth two angels in white sitting,
12 sai ta ga waɗansu mala’iku biyu saye da fararen tufafi, zaune a inda dā gawar Yesu take, ɗaya wajen kai ɗayan kuma wajen ƙafafu.
one at the head, and one at the feet, where the body of Jesus had lain.
13 Suka tambaye ta cewa, “Mace, don me kike kuka?” Ta ce, “Sun ɗauke Ubangijina, ban kuma san inda suka ajiye shi ba.”
And they said to her, Woman, why dost thou weep? She saith unto them, Because they have taken away my Lord, and I know not where they have laid Him.
14 Da ta faɗin haka, sai ta juya ta ga Yesu tsaye, sai dai ba tă gane cewa Yesu ne ba.
And having said this, she turned back, and saw Jesus standing, and knew not that it was Jesus.
15 Sai ya ce, “Mace, don me kike kuka? Wa kike nema?” Ta yi tsammani shi ne mai aikin lambun, sai ta ce, “Ranka yă daɗe, in kai ne ka ɗauke shi, gaya mini inda ka ajiye shi, in je in ɗauke shi.”
Then said Jesus to her, Woman, why dost thou weep? whom dost thou seek? She thinking that it was the gardener, saith to Him, Sir, if thou hast carried Him hence, tell me where thou hast laid Him, and I will take Him away.
16 Yesu ya ce mata, “Maryamu.” Sai ta juya wajensa ta ɗaga murya ta ce da Arameyanci, “Rabboni!” (Wanda yake nufin “Malam”).
Jesus saith unto her, Mary: and she turned herself and said unto Him, Rabboni, that is to say, Master.
17 Yesu ya ce, “Kada ki riƙe ni, gama ban riga na koma wajen Uba tukuna ba. A maimako, ki tafi wajen’yan’uwana ki gaya musu, ‘Ina komawa wajen Ubana da Ubanku, wajen Allahna da kuma Allahnku.’”
Jesus saith unto her, Touch me not now; for I am not yet ascended to my Father; but go directly to my brethren, and tell them, "I am to ascend to my Father and your Father, and to my God and your God."
18 Sai Maryamu Magdalin ta wajen almajiran da labari cewa, “Na ga Ubangiji!” Ta kuma gaya musu cewa ya faɗa mata waɗannan abubuwa.
So Mary Magdalene came and told the disciples, that she had seen the Lord, and that He had said these things to her.
19 Da Yamman ranar farko ta mako, sa’ad da almajiran suna tare, ƙofofi kuma suna a kulle saboda tsoron Yahudawa, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsakiyarsu ya ce, “Salama tă kasance tare da ku!”
Now the same day at evening, being the first day of the week, and the doors where the disciples were being shut, for fear of the Jews, Jesus came and stood in the midst, and saith unto them, Peace be to you.
20 Bayan ya faɗa haka, sai ya nuna musu hannuwansa da gefensa. Sai almajiran suka yi farin ciki ƙwarai da suka ga Ubangiji.
And when He had said this, He shewed them his hands and his side. The disciples therefore rejoiced when they saw the Lord.
21 Sai Yesu ya sāke ce musu, “Salama tă kasance tare da ku! Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka ni ma ina aikan ku.”
Then said Jesus unto them again, Peace be to you. As my Father sent me, even so send I you.
22 Da wannan sai ya hura musu numfashinsa ya ce, “Ku karɓi Ruhu Mai Tsarki.
And when He said this, He breathed upon them, and saith unto them, Receive ye the holy Spirit:
23 Duk wanda kuka gafarta wa zunubansa, an gafarta masa ke nan. Duk wanda ba ku gafarta wa ba kuwa, ba a gafarta masa ba ke nan.”
and whose soever sins ye remit, they are remitted unto them; but whose soever sins ye retain, they are retained.
24 Toma kuwa (wanda ake kira Didaimus), ɗaya daga cikin Sha Biyun, ba ya tare da almajiran sa’ad da Yesu ya zo.
But Thomas called Didymus, one of the twelve, was not with them when Jesus came.
25 Saboda haka sauran almajiran suka ce masa, “Ai, mun ga Ubangiji!” Amma ya ce musu, “Ina, ai, sai na ga ramin ƙusa a hannuwansa na sa yatsata a inda ƙusoshi suka kasance, na kuma sa hannuna a gefensa, in ba haka ba, ba zan gaskata ba.”
The other disciples therefore told him, We have seen the Lord. But he said unto them, Except I see in his hands the mark of the nails, and put my finger into the place of the nails, and my hand into his side, I will not believe.
26 Bayan mako guda, har wa yau almajiransa suna cikin gidan, Toma kuwa yana tare da su. Ko da yake ƙofofi suna kulle, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsakiyarsu ya ce, “Salama tă kasance tare da ku!”
And after eight days his disciples were again within, and Thomas with them: and Jesus came (the doors being shut as before) and stood in the midst, and said, Peace be to you.
27 Sa’an nan ya ce wa Toma, “Sa yatsarka nan; dubi hannuwana. Miƙa hannunka ka sa a gefena. Ka daina shakka ka gaskata.”
Then saith He to Thomas, Reach hither thy finger, and behold my hands, and reach hither thy hand, and put it into my side; and be not incredulous, but believing.
28 Toma ya ce masa, “Ya Ubangijina da Allahna!”
And Thomas answered, and said, "My Lord and my God."
29 Sai Yesu ya ce masa, “Wato ka gaskata saboda ka gan ni ne, masu albarka ne waɗanda ba su gan ni ba, amma suka gaskata.”
Jesus saith unto him, Thomas, because thou hast seen me, thou hast believed: blessed are they that have not seen, and yet have believed.
30 Yesu ya yi waɗansu abubuwan banmamaki da yawa a gaban almajiransa da ba a rubuta a wannan littafi ba.
And indeed Jesus wrought many other signs also in the presence of his disciples, which are not written in this book:
31 An dai rubuta waɗannan ne don ku gaskata Yesu ne Kiristi, Ɗan Allah kuma ta wurin gaskatawa ku sami rai a cikin sunansa.
but these things are written, that ye may believe, that Jesus is the Christ, the Son of God; and that believing ye may have life through his name.

< Yohanna 20 >