< Yohanna 20 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, tun da sauran duhu, Maryamu Magdalin ta tafi kabarin ta kuwa tarar an kawar da dutsen daga bakin kabarin.
But on the first day of the week Mary the Magdalene cometh early, while it was yet dark, to the tomb, and seeth that the stone had been taken away from the tomb.
2 Sai ta zo da gudu wajen Siman Bitrus da ɗayan almajirin, wanda Yesu yake ƙauna, ta ce, “Sun ɗauke Ubangiji daga kabarin, ba mu kuma san inda suka sa shi ba!”
She runneth therefore, and cometh to Simon Peter, and to the other disciple, whom Jesus loved, and saith to them, They have taken away the Lord out of the tomb, and we know not where they have laid him.
3 Sai Bitrus da almajirin nan suka nufi kabarin.
Peter therefore went forth, and the other disciple, and they set out for the tomb.
4 Dukansu biyu suna gudu, amma ɗayan almajirin ya tsere wa Bitrus ya kuma fara kai kabarin.
And they ran both together; and the other disciple outran Peter, and came first to the tomb.
5 Ya sunkuya ya duba ciki ya ga ƙyallayen lilin ne kwance a can amma bai shiga ba.
And stooping down, he seeth the linen cloths lying; but he did not go in.
6 Sa’an nan Siman Bitrus, wanda yake bayansa, ya iso ya kuwa wuce cikin kabarin. Ya ga ƙyallayen lilin kwance a can,
Then cometh also Simon Peter following him, and he went into the tomb; and he beholdeth the linen cloths lying,
7 haka ma zanen binnewar da aka naɗe kan Yesu da shi. Zanen a naɗe yake shi kaɗai, a keɓe da lilin ɗin.
and the napkin that was about his head, not lying with the linen cloths, but folded up in a place by itself.
8 A ƙarshe sai almajirin nan, wanda ya kai kabarin da farko, shi ma ya shiga. Ya gani ya kuma gaskata.
Then therefore went in also the other disciple, who came first to the tomb; and he saw, and believed.
9 (Har yanzu ba su fahimci Nassin nan da ya ce lalle ne Yesu yă tashi daga matattu ba.)
For not even yet did they know the Scripture, that he must rise from the dead.
10 Sai almajiran suka koma zuwa inda suke zama.
So the disciples went away again to their home.
11 Maryamu kuwa ta tsaya a bakin kabarin daga waje tana kuka. Da tana cikin kuka, sai ta sunkuya ta leƙa cikin kabarin,
But Mary was standing without by the tomb weeping. And as she wept, she stooped down into the tomb,
12 sai ta ga waɗansu mala’iku biyu saye da fararen tufafi, zaune a inda dā gawar Yesu take, ɗaya wajen kai ɗayan kuma wajen ƙafafu.
and beholdeth two angels in white sitting, one at the head, and one at the feet, where the body of Jesus had lain.
13 Suka tambaye ta cewa, “Mace, don me kike kuka?” Ta ce, “Sun ɗauke Ubangijina, ban kuma san inda suka ajiye shi ba.”
And they say to her, Woman, why dost thou weep? She saith to them, Because they have taken away my Lord, and I know not where they have laid him.
14 Da ta faɗin haka, sai ta juya ta ga Yesu tsaye, sai dai ba tă gane cewa Yesu ne ba.
Having said this, she turned back, and beheld Jesus standing; and knew not that it was Jesus.
15 Sai ya ce, “Mace, don me kike kuka? Wa kike nema?” Ta yi tsammani shi ne mai aikin lambun, sai ta ce, “Ranka yă daɗe, in kai ne ka ɗauke shi, gaya mini inda ka ajiye shi, in je in ɗauke shi.”
Jesus saith to her, Woman, why dost thou weep? whom dost thou seek? She, supposing that it was the gardener, saith to him, Sir, if thou hast borne him hence, tell me where thou hast laid him, and I will take him away.
16 Yesu ya ce mata, “Maryamu.” Sai ta juya wajensa ta ɗaga murya ta ce da Arameyanci, “Rabboni!” (Wanda yake nufin “Malam”).
Jesus saith to her, Mary! She turned and saith to him in Hebrew, Rabboni! Which signifieth, Teacher!
17 Yesu ya ce, “Kada ki riƙe ni, gama ban riga na koma wajen Uba tukuna ba. A maimako, ki tafi wajen’yan’uwana ki gaya musu, ‘Ina komawa wajen Ubana da Ubanku, wajen Allahna da kuma Allahnku.’”
Jesus saith to her, Touch me not; for I have not yet ascended to the Father; but go to my brethren, and say to them, I ascend to my Father and your Father, and my God and your God.
18 Sai Maryamu Magdalin ta wajen almajiran da labari cewa, “Na ga Ubangiji!” Ta kuma gaya musu cewa ya faɗa mata waɗannan abubuwa.
Mary the Magdalene cometh, bringing word to the disciples that she had seen the Lord, and that he had said these things to her.
19 Da Yamman ranar farko ta mako, sa’ad da almajiran suna tare, ƙofofi kuma suna a kulle saboda tsoron Yahudawa, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsakiyarsu ya ce, “Salama tă kasance tare da ku!”
When therefore it was evening on that day, which was the first day of the week, and the doors where the disciples were had been shut for fear of the Jews, Jesus came and stood in the midst, and said to them, Peace be to you!
20 Bayan ya faɗa haka, sai ya nuna musu hannuwansa da gefensa. Sai almajiran suka yi farin ciki ƙwarai da suka ga Ubangiji.
And having said this, he showed them his hands and his side. The disciples therefore were glad, when they saw the Lord.
21 Sai Yesu ya sāke ce musu, “Salama tă kasance tare da ku! Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka ni ma ina aikan ku.”
Then he said to them again, Peace be to you! As the Father hath sent me, I also send you.
22 Da wannan sai ya hura musu numfashinsa ya ce, “Ku karɓi Ruhu Mai Tsarki.
And having said this, he breathed on them, and saith to them, Receive the Holy Spirit.
23 Duk wanda kuka gafarta wa zunubansa, an gafarta masa ke nan. Duk wanda ba ku gafarta wa ba kuwa, ba a gafarta masa ba ke nan.”
Whosever sins ye remit, they are remitted to them; whosever ye retain, they are retained.
24 Toma kuwa (wanda ake kira Didaimus), ɗaya daga cikin Sha Biyun, ba ya tare da almajiran sa’ad da Yesu ya zo.
But Thomas, one of the twelve, called Didymus, was not with them when Jesus came.
25 Saboda haka sauran almajiran suka ce masa, “Ai, mun ga Ubangiji!” Amma ya ce musu, “Ina, ai, sai na ga ramin ƙusa a hannuwansa na sa yatsata a inda ƙusoshi suka kasance, na kuma sa hannuna a gefensa, in ba haka ba, ba zan gaskata ba.”
The other disciples therefore said to him, We have seen the Lord. But he said to them, Unless I see in his hands the print of the nails, and put my finger into the place of the nails, and put my hand into his side, I shall not believe.
26 Bayan mako guda, har wa yau almajiransa suna cikin gidan, Toma kuwa yana tare da su. Ko da yake ƙofofi suna kulle, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsakiyarsu ya ce, “Salama tă kasance tare da ku!”
And after eight days the disciples were again within, and Thomas with them. Jesus cometh, the doors being shut, and stood in the midst, and said, Peace be to you!
27 Sa’an nan ya ce wa Toma, “Sa yatsarka nan; dubi hannuwana. Miƙa hannunka ka sa a gefena. Ka daina shakka ka gaskata.”
Then he saith to Thomas, Reach hither thy finger, and behold my hands, and reach forth thy hand, and put it into my side; and be not faithless, but believing.
28 Toma ya ce masa, “Ya Ubangijina da Allahna!”
Thomas answered and said to him, My Lord and my God!
29 Sai Yesu ya ce masa, “Wato ka gaskata saboda ka gan ni ne, masu albarka ne waɗanda ba su gan ni ba, amma suka gaskata.”
Jesus saith to him, Because thou hast seen me, thou hast believed; blessed are they who have not seen, and yet have believed.
30 Yesu ya yi waɗansu abubuwan banmamaki da yawa a gaban almajiransa da ba a rubuta a wannan littafi ba.
Many other signs did Jesus in the presence of his disciples, which are not written in this book.
31 An dai rubuta waɗannan ne don ku gaskata Yesu ne Kiristi, Ɗan Allah kuma ta wurin gaskatawa ku sami rai a cikin sunansa.
But these have been written, that ye may believe that Jesus is the Christ the Son of God, and that believing ye may have life in his name.

< Yohanna 20 >