< Yohanna 2 >

1 A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can,
I KE kolu o ka la, he ahaaina mare ma Kana i Galilaia; ilaila no hoi ka makuwahine o Iesu.
2 aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren.
Ua oleloia o Iesu, a me ua haumana ana, e hele i ua ahaaina mare la.
3 Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
A nele i ka waina, i aku la ka makuwahine o Iesu ia ia, Aohe o lakou waina.
4 Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”
Olelo mai la Iesu ia ia, E ka wahine, o ke aha la ia ia kaua? aole i hiki mai ko'u manawa.
5 Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
Olelo aka la kona makuwahine i na kauwa, O ka mea ana e olelo mai ai ia oukou, oia ka oukou e hana'i.
6 Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.
E waiho ana malaila na ipuwai pohaku eono, no ka hoomaemae ana o ka poe Iudaio, he iwakalua kumamahiku, he kanaha paha na galani e piha ai ka kekahi, ka kekahi.
7 Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.
I mai la o Iesu ia lakou, E hoopiha i na ipuwai i ka wai. Hoopina iho lakou i ua mau mea la, a piha loa.
8 Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.” Suka yi haka.
I mai hoi oia ia lakou, E hookahe mai ano, a lawe aku i ka lunaahaaina. A lawe aku la lakou.
9 Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya
A i ka hoao ana o ka lunaahaaina i ka wai i hooliloia i waina, aole oia i ike i kahi i loaa'i, (o na kauwa, nana i hookahe ka wai, ka i ike, ) kahea aku la ka lunaahaaina i ke kanemare,
10 ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”
I aku la ia ia, Lawe mua mai no kela kanaka keia kanaka i ka waina maikai, a nui ko lakou inu ana, alaila i ka waina ino: ua malama ka oe i ka waina maikai, a keia manawa.
11 Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.
Hana iho la o Iesu i keia hana mana mua ma Kana i Galilaia, a hoike ae la ia i kona nani; a manaoio aku la kana poe haumana ia ia.
12 Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna’yan kwanaki.
Mahope mai o keia, iho aku la ia i Kaperenauma, oia a me kona makuwahine, a me kona mau hoahanau, a me kana poe haumana, aohe nui na la i noho ai lakou malaila,
13 Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima.
Ua kokoke mai ka moliaola a na Iudaio; a pii aku la o Iesu i Ierusalema,
14 A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi.
A loaa aku la ia ia ka poe e kuai ana i na bipi, a me na hipa, a me na manu nunu, a me ka poe kuai kala, e noho ana iloko o ka luakini.
15 Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu.
Hana iho la ia i mea hahau no na kaula liilii, a hookuke aku la oia ia lakou a pau iwaho o ka luakini, a me na hipa, a me na bipi; lu aku la i na kala o ka poe kuai kala, a hookahuli i na papa;
16 Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!”
Olelo mai la ia i ka poe kuai mana nunu, E lawe ae i keia mau mea mai keia wahi aku; mai hoolilo oukou i ka hale o ko'u Makua i hale kuai.
17 Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”
Hoomanao iho la kana poe haumana i ka mea i palapalaia, O ka manao nui i kou hale ka mea e ai mai nei ia'u.
18 Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”
Ninau aku la na Iudaio ia ia, i aku la, Heaha ka hoailona au e hoike mai ai ia makou, i hana ai oe i neia mau mea?
19 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”
Olelo mai la o Iesu ia lakou, E wawahi oukou i keia luakini, a e kukulu hou aku au ia i na la ekolu.
20 Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?”
Alaila olelo aku la na Iudaio, Hookahi kanaha makahiki a me kumamaono ka hana ana o keia luakini, a e kukulu hou auei oe ia mea i na la ekolu?
21 Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne.
O kona kino iho no ka luakini ana i olelo mai ai.
22 Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.
A ala mai oia mai ka make mai, hoomanao iho la kana poe haumana, ua olelo oia i keia mea; a manaoio iho la lakou i ka palapala hemolele, a me ka olelo a Iesu i olelo mai ai.
23 To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
A i kona noho ana ma Ierusalema i ka ahaaina moliaola, he nui loa na mea i manaoio i kona inoa, i ko lakou ike aua i na hana mana ana i hana'i,
24 Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
Aka, aole o Iesu i kuu aku ia ia iho no lakou, no ka mea, ua ike no oia ia lakou a pau,
25 Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.
Aole ona hemahema e pono ai ke hoike aku kekahi ia ia i ko ke kanaka: no ka mea, ua ike no ia i ko loko o kanaka.

< Yohanna 2 >