< Yohanna 2 >

1 A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can,
Trois jours après, on faisait des noces à Cana en Galilée, et la mère de Jésus y était.
2 aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren.
Et Jésus fut aussi convié aux noces avec ses disciples.
3 Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
Le vin ayant manqué, la mère de Jésus lui dit: Ils n'ont plus de vin.
4 Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”
Jésus lui répondit: Femme, qu'y a-t-il entre moi et toi? Mon heure n'est pas encore venue.
5 Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
Sa mère dit à ceux qui servaient: Faites tout ce qu'il vous dira.
6 Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.
Or, il y avait là six vaisseaux de pierre, placés pour la purification des Juifs, et contenant chacun deux ou trois mesures.
7 Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.
Jésus leur dit: Remplissez d'eau ces vaisseaux; et ils les remplirent jusqu'au haut.
8 Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.” Suka yi haka.
Et il leur dit: Puisez-en maintenant, et portez-en au chef du festin. Et ils le firent.
9 Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya
Quand le chef du festin eut goûté l'eau changée en vin (or, il ne savait pas d'où venait ce vin, mais les serviteurs qui avaient puisé l'eau le savaient), il appela l'époux,
10 ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”
Et lui dit: Tout homme sert d'abord le bon vin, et ensuite le moins bon, après qu'on a beaucoup bu; mais toi, tu as gardé le bon vin jusqu'à présent.
11 Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.
Jésus fit ce premier miracle à Cana de Galilée, et il manifesta sa gloire; et ses disciples crurent en lui.
12 Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna’yan kwanaki.
Après cela, il descendit à Capernaüm avec sa mère, ses frères et ses disciples; et ils n'y demeurèrent que peu de jours;
13 Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima.
Et la Pâque des Juifs était proche, et Jésus monta à Jérusalem.
14 A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi.
Et il trouva dans le temple ceux qui vendaient des taureaux, des brebis et des pigeons, avec les changeurs qui y étaient assis.
15 Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu.
Et ayant fait un fouet de cordes, il les chassa tous du temple, et les brebis et les taureaux; il répandit la monnaie des changeurs, et renversa leurs tables.
16 Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!”
Et il dit à ceux qui vendaient les pigeons: Otez cela d'ici, et ne faites pas de la maison de mon Père une maison de marché.
17 Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”
Alors ses disciples se souvinrent qu'il est écrit: Le zèle de ta maison m'a dévoré.
18 Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”
Les Juifs, prenant la parole, lui dirent: Quel signe nous montres-tu pour agir de la sorte?
19 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”
Jésus répondit et leur dit: Abattez ce temple, et je le relèverai dans trois jours.
20 Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?”
Les Juifs lui dirent: On a été quarante-six ans à bâtir ce temple, et tu le relèveras dans trois jours?
21 Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne.
Mais il parlait du temple de son corps.
22 Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.
Après donc qu'il fut ressuscité des morts, ses disciples se souvinrent qu'il leur avait dit cela; et ils crurent à l'Écriture et à cette parole que Jésus avait dite.
23 To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
Pendant qu'il était à Jérusalem, à la fête de Pâque, plusieurs crurent en son nom, voyant les miracles qu'il faisait.
24 Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
Mais Jésus ne se fiait point à eux, parce qu'il les connaissait tous,
25 Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.
Et qu'il n'avait pas besoin qu'on lui rendît témoignage d'aucun homme, car il savait de lui-même ce qui était dans l'homme.

< Yohanna 2 >