< Yohanna 2 >
1 A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can,
And on the third day after, there was a marriage at Cana of Galilee: and the mother of Jesus was there.
2 aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren.
And Jesus and his disciples were invited to the wedding.
3 Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
And the wine falling short, the mother of Jesus saith unto Him, They have no wine.
4 Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”
Jesus saith unto her, Woman, what have I to do with thee? my time is not yet come.
5 Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
His mother saith to the servants, Whatsoever he ordereth you to do, do it.
6 Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.
And there were six stone waterpots, placed according to the custom of purifying among the Jews, containing each about two or three firkins.
7 Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.
Jesus saith unto them, Fill the water-pots with water: and they filled them up to the brim.
8 Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.” Suka yi haka.
And he saith unto them, Draw out now, and carry it to the master of the feast. And they carried it to him.
9 Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya
And when the manager of the feast had tasted the water which was made wine, and knew not whence it was, (but the servants, that drew the water, knew, ) he called the bride-groom,
10 ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”
and saith unto him, Every man sets out good wine at first, and when they have drank plentifully, then that which is worse; but thou hast keep the good wine till now.
11 Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.
This beginning of his miracles Jesus wrought at Cana of Galilee, and made manifest his glory: and his disciples believed on Him.
12 Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna’yan kwanaki.
After this He went down to Capernaum, He and his mother, and his brethren, and his disciples: but they staid there not many days.
13 Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima.
For the passover of the Jews was near, and Jesus went up to Jerusalem. And He found in the temple those that sold oxen,
14 A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi.
and sheep, and doves, and the money changers sitting:
15 Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu.
and having made a whip of small cords He drove them all, out of the temple; with the sheep and the oxen: and He poured out the changers money, and threw down the tables.
16 Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!”
And said to them that sold doves, Take away these things from hence, and make not my Father's house an house of traffick.
17 Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”
And his disciples remembered that it is written, The zeal of thine house hath eaten me up.
18 Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”
The Jews therefore answered and said unto Him, What sign dost thou shew us, seeing thou dost these things?
19 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”
Jesus answered and said unto them, Destroy this temple, and in three days I will raise it up again: then said the Jews,
20 Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?”
Forty and six years has this temple been in building, and wilt thou raise it up in three days? but He spake of the temple of his body.
21 Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne.
Therefore when he was risen from the dead,
22 Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.
his disciples remembered, that He had said this to them: and they believed the scripture, and the word which Jesus had said.
23 To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
And when he was in Jerusalem at the passover on the feast-day, many believed in his name, seeing his miracles, which He wrought.
24 Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
But Jesus did not trust Himself to them;
25 Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.
for He knew all men, and He had no need that any should testify concerning man; for He knew what was in man.