< Yohanna 2 >
1 A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can,
And on the third day there was a marriage in Cana of Galilee; and the mother of Jesus was there.
2 aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren.
And both Jesus and his disciples were invited to the marriage.
3 Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
And the wine having failed, the mother of Jesus said to him: They have no wine.
4 Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”
Jesus said to her: Woman, what have I to do with you? my hour has not yet come.
5 Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
His mother said to the servants: Whatever he says to you, do.
6 Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.
Now, according to the Jewish custom of purifying, six water-pots of stone had been set there, containing each two or three baths.
7 Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.
Jesus said to them: Fill the water-pots with water. And they filled them to the brim.
8 Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.” Suka yi haka.
And he said to them: Draw out now, and carry it to the governor of the feast. And they carried it.
9 Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya
When the governor of the feast had tasted the water that had been made wine, (and he knew not whence it was, but the servants that had drawn the water knew, ) the governor of the feast called the bridegroom, and said to him:
10 ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”
Every man sets out the good wine first, and when they have drunk freely, then that which is inferior; but you have kept the good wino till now.
11 Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.
This beginning of signs Jesus made in Cana of Galilee, and manifested his glory; and his disciples believed on him.
12 Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna’yan kwanaki.
After this he went down to Capernaum, he and his mother and his brothers and his disciples. And they continued there not many days.
13 Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima.
And the passover of the Jews was near, and Jesus went up to Jerusalem.
14 A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi.
And he found in the temple those who were selling oxen and sheep and doves, and the money-changers sitting.
15 Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu.
And when he had made a whip of cords, he drove them all out of the temple, the sheep also, and the oxen, and he poured out the money of the money-changers, and overthrew their tables;
16 Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!”
and said to those who sold doves: Take these things hence; make not my Father’s house a house of merchandise.
17 Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”
And his disciples remembered that it was written, Zeal for thy house has eaten me up.
18 Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”
Then answered the Jews and said to him: What sign do you show us, seeing that you do these things?
19 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”
Jesus answered and said to them: Destroy this temple, and I will raise it up in three days.
20 Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?”
Then the Jews said to him: Forty and six years was this temple in building, and will you rebuild it in three days?
21 Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne.
But he spoke of the temple of his body.
22 Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.
When, therefore, he was raised from the dead, his disciples remembered that he had said this. And they believed the scripture, and the word that Jesus had spoken.
23 To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
And while he was in Jerusalem, during the feast of passover, many believed on his name, because they saw the signs that he did.
24 Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
But Jesus did not trust himself to them, because he knew all men,
25 Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.
and had no need that any one should testify of man, for he himself knew what was in man.