< Yohanna 2 >
1 A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can,
Trećeg dana bijaše svadba u Kani Galilejskoj. Bila ondje Isusova majka.
2 aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren.
Na svadbu bijaše pozvan i Isus i njegovi učenici.
3 Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
Kad ponesta vina, Isusu će njegova majka: “Vina nemaju.”
4 Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”
Kaže joj Isus: “Ženo, što ja imam s tobom? Još nije došao moj čas!”
5 Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
Nato će njegova mati poslužiteljima: “Što god vam rekne, učinite!”
6 Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.
A bijaše ondje Židovima za čišćenje šest kamenih posuda od po dvije do tri mjere.
7 Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.
Kaže Isus poslužiteljima: “Napunite posude vodom!” I napune ih do vrha.
8 Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.” Suka yi haka.
Tada im reče: “Zagrabite sada i nosite ravnatelju stola.” Oni odnesu.
9 Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya
Kad okusi vodu što posta vinom, a nije znao odakle je - znale su sluge koje zagrabiše vodu - ravnatelj stola pozove zaručnika
10 ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”
i kaže mu: “Svaki čovjek stavlja na stol najprije dobro vino, a kad se ponapiju, gore. Ti si čuvao dobro vino sve do sada.”
11 Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.
Tako, u Kani Galilejskoj, učini Isus prvo znamenje i objavi svoju slavu te povjerovaše u njega njegovi učenici.
12 Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna’yan kwanaki.
Nakon toga siđe sa svojom majkom, s braćom i sa svojim učenicima u Kafarnaum. Ondje ostadoše nekoliko dana.
13 Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima.
Blizu bijaše židovska Pasha. Stoga Isus uziđe u Jeruzalem.
14 A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi.
U Hramu nađe prodavače volova, ovaca i golubova i mjenjače gdje sjede.
15 Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu.
I načini bič od užeta te ih sve istjera iz Hrama zajedno s ovcama i volovima. Mjenjačima rasu novac i stolove isprevrta,
16 Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!”
a prodavačima golubova reče: “Nosite to odavde i ne činite od kuće Oca mojega kuću trgovačku.”
17 Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”
Prisjetiše se njegovi učenici da je pisano: Izjeda me revnost za Dom tvoj.
18 Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”
Nato se umiješaju Židovi i upitaju ga: “Koje nam znamenje možeš pokazati da to smiješ činiti?”
19 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”
Odgovori im Isus: “Razvalite ovaj hram i ja ću ga u tri dana podići.”
20 Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?”
Rekoše mu nato Židovi: “Četrdeset i šest godina gradio se ovaj Hram, a ti da ćeš ga u tri dana podići?”
21 Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne.
No on je govorio o hramu svoga tijela.
22 Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.
Pošto uskrsnu od mrtvih, prisjetiše se njegovi učenici da je to htio reći te povjerovaše Pismu i besjedi koju Isus reče.
23 To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
Dok je boravio u Jeruzalemu o blagdanu Pashe, mnogi povjerovaše u njegovo ime promatrajući znamenja koja je činio.
24 Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
No sam se Isus njima nije povjeravao jer ih je sve dobro poznavao
25 Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.
i nije trebalo da mu tko daje svjedočanstvo o čovjeku: ta sam je dobro znao što je u čovjeku.