< Yohanna 19 >
1 Sa’an nan Bilatus ya tafi da Yesu ya kuma sa aka yi masa bulala.
Siis Pilaatus võttis Jeesuse ja lasi teda piitsutada.
2 Sai sojojin suka tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa a kā, suka kuma yafa masa wata riga mai ruwan shunayya.
Sõdurid tegid okaspõõsast krooni ja panid selle talle pähe ning asetasid talle õlgadele purpurrüü.
3 Suka yi ta zuwa wurinsa suna cewa, “Ranka yă daɗe, sarkin Yahudawa!” Suna ta marinsa a fuska.
Ikka ja jälle läksid nad tema juurde ja ütlesid: „Ole tervitatud, juutide kuningas!“ja lõid talle vastu nägu.
4 Bilatus kuwa ya sāke fitowa ya ce wa Yahudawa, “Ga shi, zan fito muku da shi don ku san cewa ban same shi da wani abin zargi ba.”
Pilaatus läks veel kord välja ja ütles neile: „Ma toon ta siia välja teie juurde, et te teaks, et ma ei mõista teda süüdi üheski kuriteos.“
5 Sa’ad da Yesu ya fito sanye da rawanin ƙayar da kuma riga mai ruwan shunayya, sai Bilatus ya ce musu, “Ga mutumin!”
Siis Jeesus tuli välja, okaskroon peas ja purpurrüü üll. „Vaadake, siin on see inimene, “ütles Pilaatus.
6 Nan da nan da manyan firistoci da ma’aikatansu suka gan shi, sai suka yi ihu suka ce, “A gicciye! A gicciye!” Amma Bilatus ya amsa ya ce, “Ku, ku ɗauke shi ku gicciye. Ni dai ban same shi da wani abin zargi ba.”
Kui ülempreestrid ja valvurid nägid Jeesust, karjusid nad: „Löö ta risti! Löö ta risti!“„Võtke teie ja lööge ta risti, “vastas Pilaatus. „Mina ei mõista teda süüdi.“
7 Yahudawa dai suka nace suna cewa, “Mu fa muna da doka, kuma bisa ga dokar dole yă mutu domin ya mai da kansa Ɗan Allah.”
Juudi juhid vastasid: „Meil on seadus ja selle seaduse järgi peab ta surema, sest ta on väitnud, et on Jumala Poeg.“
8 Da Bilatus ya ji haka, sai tsoro ya ƙara kama shi,
Kui Pilaatus seda kuulis, kartis ta veel rohkem kui enne
9 sai ya sāke koma cikin fada. Ya tambayi Yesu, “Daga ina ka fito?” Amma Yesu bai amsa masa ba.
ja läks tagasi maavalitseja paleesse. Ta küsis Jeesuselt: „Kust sa pärit oled?“Aga Jeesus ei vastanud.
10 Bilatus ya ce, “Ba za ka yi mini magana ba? Ba ka san cewa ina da ikon sakinka, ko gicciye ka ba?”
„Kas sa keeldud minuga rääkimast?“küsis Pilaatus talt. „Kas sa ei saa aru, et mul on võim sind vabaks lasta või risti lüüa?“
11 Yesu ya amsa ya ce, “Ba ka da wani iko a kaina, in ba a ba ka daga sama ba. Saboda haka wanda ya bashe ni gare ka, ya fi na zunubi.”
„Sul ei oleks minu üle mingit võimu, kui seda ei oleks sulle antud ülalt, “vastas Jeesus. „Seepärast on see, kes mu sinu kätte andis, suuremas patus süüdi.“
12 Daga nan fa, Bilatus ya yi nemi yă saki Yesu, sai dai Yahudawa suka yi ta ihu suna cewa, “In ka saki wannan mutum, kai ba abokin Kaisar ba ne. Duk wanda ya ɗauka kansa a matsayin sarki, ai, yana gāba da Kaisar ne.”
Kui Pilaatus seda kuulis, üritas ta Jeesust vabaks lasta, kuid juudi juhid karjusid: „Kui sa selle mehe vabaks lased, ei ole sa keisri sõber. Kes laseb vabaks end kuningaks tõstva inimese, see mässab keisri vastu.“
13 Da Bilatus ya ji haka, sai ya fito da Yesu, ya kuma zauna a kujerar shari’ar da ake ce da shi Daɓen Dutse (wanda a harshen Arameyik ana ce da shi Gabbata).
Kui Pilaatus seda kuulis, tõi ta Jeesuse välja ja istus kohtunikutoolile kohas, mida nimetatakse Kivisillutiseks (heebrea keeles Gabbata).
14 Ranar Shirye-shiryen Makon Bikin Ƙetarewa ce kuwa, wajen sa’a ta shida. Sai Bilatus ya ce wa Yahudawa, “Ga sarkinku.”
Oli umbes paasapühale eelneva valmistuspäeva keskpäev. „Vaadake, siin on teie kuningas, “ütles ta juutidele.
15 Amma suka yi ihu suka ce, “A yi da shi! A yi da shi! A gicciye shi!” Bilatus ya ce, “A! In gicciye sarkinku?” Sai manyan firistoci suka amsa suka ce, “Mu dai, ba mu da wani sarki sai Kaisar.”
„Hukka ära! Hukka ära! Löö ta risti!“karjusid nad. „Kas tahate, et löön teie kuninga risti?“küsis Pilaatus. „Meie ainus kuningas on keiser, “vastasid ülempreestrid.
16 A ƙarshe Bilatus ya ba da shi gare su a gicciye shi. Saboda haka sojoji suka tafi da Yesu.
Nii andis ta Jeesuse nende kätte, et ta risti lüüa.
17 Ɗauke da gicciyensa, ya kuwa fita zuwa wurin Ƙoƙon Kai (wanda a harshen Arameya ana ce da shi Golgota).
Nad viisid ära Jeesuse, kes kandis ise oma risti, ja läksid välja paika, mida nimetatakse Pealuuks (heebrea keeles Kolgata).
18 Nan suka gicciye shi tare da waɗansu mutum biyu, ɗaya a kowane gefe da Yesu a tsakiya.
Nad lõid ta seal risti, ja veel kaks meest koos temaga, ühe kummalegi poole, nii et Jeesus jäi nende vahele.
19 Bilatus ya sa aka rubuta wata sanarwa aka kafa a kan gicciyen. Abin da aka rubuta kuwa shi ne, Yesu Banazare, Sarkin Yahudawa.
Pilaatus oli teinud sildi ja pani selle risti külge. Sellele oli kirjutatud: „Naatsareti Jeesus, juutide kuningas.“
20 Yahudawa da yawa suka karanta wannan sanarwa, gama inda aka gicciye Yesu yana kusa da birni. An kuwa rubuta sanarwar da Arameyanci, Romanci da kuma Girik.
Paljud lugesid seda silt, sest koht, kus Jeesus risti löödi, asus linna lähedal, ning silt oli kirjutatud heebrea, ladina ja kreeka keeles.
21 Sai manyan firistocin Yahudawa suka ce, “A’a! Kada ka rubuta, ‘Sarkin Yahudawa,’ ka dai rubuta, wannan mutum ya ce shi sarkin Yahudawa ne.”
Siis tulid ülempreestrid Pilaatuse juurde ja palusid teda: „Ära kirjuta „juutide kuningas“, vaid „see mees ütles, et on juutide kuningas“.“
22 Bilatus ya amsa ya ce, “Abin da na rubuta, na rubuta.”
Pilaatus vastas: „Kirjutasin seda, mida kirjutasin.“
23 Da sojojin suka gicciye Yesu, sai suka ɗibi tufafinsa suka kasa kashi huɗu, kowanne ya ɗauki kashi ɗaya. Suka kuma ɗauki taguwarsa, taguwar kuwa ba ɗinki, saƙa ɗaya ce gudanta daga sama har ƙasa.
Kui sõdurid olid Jeesuse risti löönud, võtsid nad tema riided ja jagasid neljaks, et iga sõdur saaks oma osa. Seal oli ka tema kuub, mis oli ühest tükist kootud, ilma õmblusteta.
24 Sai suka ce wa juna, “Kada mu yage ta, sai dai mu jefa ƙuri’a a kanta mu ga wanda zai ci.” Wannan ya faru ne don a cika nassin da ya ce, “Suka rarraba tufafina a junansu, suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigata.” Abin da sojojin suka yi ke nan.
Seepärast ütlesid nad üksteisele: „Ärme rebi seda katki, vaid otsustame täringut heites, kes selle endale saab.“Nii täitus see, mis on Pühakirjas öeldud: „Nad jaotavad mu rõivad omavahel ja veeretavad täringut mu kehakatte pärast.“
25 To, tsaye kusa da gicciyen Yesu kuwa akwai mahaifiyarsa, tare da’yar’uwar mahaifiyarsa, Maryamu matar Kilofas, da kuma Maryamu Magdalin.
Seda need sõdurid tegidki. Risti lähedal olid Jeesuse ema ja tema ema õde, Kloopase naine Maarja ja Maarja Magdaleena.
26 Sa’ad da Yesu ya ga mahaifiyarsa a can, da kuma almajirin nan da yake ƙauna tsaye kusa, sai ya ce wa mahaifiyarsa, “Mace, ga ɗanki,”
Kui Jeesus nägi oma ema ja tema kõrval jüngrit, keda ta armastas, ütles ta emale: „Naine, see on sinu poeg.“
27 ga almajirin kuwa ya ce, “Ga mahaifiyarka.” Tun daga wannan lokaci fa almajirin nan ya kai ta gidansa.
Seejärel ütles ta jüngrile: „See on sinu ema.“Sellest ajast peale võttis jünger ta enda juurde.
28 Bayan haka, sanin cewa an cika kome, kuma domin a cika Nassi, sai Yesu ya ce, “Ina jin ƙishirwa.”
Jeesus mõistis nüüd, et ta oli lõpetanud kõik, mida ta oli tegema tulnud. Et täituks Pühakiri, ütles ta: „Mul on janu.“
29 To, akwai wani tulun ruwan tsami ajiye a can, saboda haka suka jiƙa soso da shi, suka soka soson a sandan itacen hizzob, suka kai bakin Yesu.
Seal seisis üks kruus veiniäädikaga; nad kastsid käsna äädikasse, panid selle iisopivarre otsa ja hoidsid seda tema huulte vastas.
30 Da ya tsotsi abin sha ɗin, sai Yesu ya ce, “An gama.” Da wannan fa, ya sunkuyar da kansa ya saki ruhunsa.
Kui Jeesus oli äädikat võtnud, ütles ta: „See on lõpetatud!“Siis langetas ta pea ja tegi viimase hingetõmbe.
31 To, ranan nan fa, ranar Shirye-shirye ce, kashegari kuma muhimmin Asabbaci ne. Domin Yahudawa ba sa so a bar jikunan a kan gicciyoyi a Asabbaci, sai suka roƙi Bilatus a kakkarye ƙafafunsu kuma sauko da jikunan.
Oli valmistuspäev, ja juudi juhid ei tahtnud ristilööduid jätta hingamispäevaks (õigupoolest oli see eriline hingamispäev) ristile, seepärast palusid nad Pilaatusel murda neil jalad, et nad saaks alla võtta.
32 Sai sojoji suka zo suka karya ƙafafun mutum na farko da aka gicciye tare da Yesu, da kuma na ɗayan.
Siis tulid sõdurid ning murdsid kahe koos Jeesusega ristilöödud mehe jalad,
33 Amma sa’ad da suka zo kan Yesu suka tarar ya riga ya mutu, ba su karya ƙafafunsa ba.
aga kui nad tulid Jeesuse juurde, nägid nad, et ta oli juba surnud, seega ei murdnud nad tema jalgu.
34 A maimako, sai ɗaya daga cikin sojojin ya soki Yesu a gefe da māshi, nan take jini da ruwa suka fito.
Kuid üks sõduritest torkas talle külje sisse oda ja välja voolas veega segunenud veri.
35 Mutumin da ya gani ɗin shi ya ba da shaida, shaidarsa kuwa gaskiya ce. Ya san gaskiya yake faɗa, yana kuma ba da shaidar domin ku ma ku gaskata.
Sellest tunnistas see, kes seda nägi, ning tema tunnistus on tõsi. Ta on kindel, et see, mida ta nägi, on tõsi, nii et ka teie võiksite seda uskuda.
36 Waɗannan abubuwa sun faru don a cika Nassi ne cewa, “Ba ko ɗaya daga cikin ƙasusuwansa da za a karya,”
Nii toimus, et läheks täide see, mis on Pühakirjas kirjutatud: „Ühtki tema luud ei murta, “
37 kuma kamar yadda wani Nassi ya ce, “Za su dubi wanda suka soka.”
ja nagu teises kohas on öeldud: „Nad näevad seda, kelle nad läbi torkasid.“
38 Bayan haka, Yusuf mutumin Arimateya ya roƙi Bilatus a ba shi jikin Yesu. Yusuf dai almajirin Yesu ne, amma a ɓoye domin yana tsoron Yahudawa. Da izinin Bilatus, ya zo ya ɗauki jikin.
Pärast seda küsis Arimaatia Joosep Pilaatuselt, kas ta võib Jeesuse surnukeha alla võtta, ning Pilaatus andis talle loa. Joosep oli Jeesuse jünger, kuid salajas, sest ta kartis juute. Niisiis tuli Joosep ja viis surnukeha ära.
39 Yana tare da Nikodimus, wannan da ya taɓa zuwa wurin Yesu da dare. Nikodimus ya zo da mur da aloyes a gauraye, wajen awo ɗari.
Temaga koos oli Nikodeemos, mees, kes oli esmalt käinud Jeesuse juures öösel. Ta tõi kaasa umbes kolmkümmend kilo mürri ja aaloe segu.
40 Da ɗaukowar jikin Yesu, sai su biyun suka nannaɗe shi tare da kayan ƙanshi a cikin ƙyallayen lilin bisa ga al’adar Yahudawa ta jana’iza.
Nad võtsid Jeesuse surnukeha ja mähkisid selle koos vürtside seguga linasesse riidesse, vastavalt juutide matmiskommetele. Selle paiga lähedal, kus Jeesus risti löödi, oli üks aed,
41 A inda aka gicciye Yesu, akwai wani lambu, a cikin lambun kuwa akwai sabon kabari, wanda ba a taɓa sa kowa ba.
ja aias oli uus, kasutamata hauakoobas.
42 Da yake ranan nan, ranar Shirye-shirye ce ta Yahudawa, kabarin kuma yana kusa, sai suka binne Yesu a can.
Kuna oli juutide valmistuspäev ja hauakoobas oli lähedal, panid nad Jeesuse sinna puhkama.