< Yohanna 18 >
1 Da ya gama addu’a, sai Yesu ya fita tare da almajiransa suka haye Kwarin Kidron. A wancan ƙetaren kuwa akwai lambun zaitun, da shi da almajiransa suka shiga ciki.
Промовивши це, Ісус вийшов із учнями Своїми на то́й бік потоку Кедро́ну, де був сад, до якого ввійшов Він та учні Його.
2 To, Yahuda, wanda ya bashe shi, ya san wurin, domin Yesu ya sha zuwa wurin da almajiransa.
Але й Юда, що видав Його, знав те місце, бо там часто збирались Ісус й Його учні.
3 Saboda haka Yahuda ya zo cikin lambun, yana jagoranta ƙungiyar sojoji da waɗansu ma’aikata daga wurin manyan firistoci da Farisiyawa. Suna riƙe da toci, fitilu da kuma makamai.
Отож Юда, узявши відділ ві́йська та службу від первосвящеників і фарисеїв, приходить туди із смолоски́пами, та з ліхтарями, та з зброєю.
4 Yesu kuwa, sane da duk abin da zai same shi, ya fito ya tambaye, su ya ce, “Wa kuke nema?”
А Ісус, усе ві́давши, що́ з Ним статися має, виходить та й каже до них: „Кого́ ви шукаєте?“
5 Suka amsa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce, “Ni ne shi.” (Yahuda kuwa wanda ya bashe shi yana nan tsaye tare da su.)
Йому відповіли: „Ісуса Назаряни́на“. Він говорить до них: „Це Я“! А стояв із ними й Юда, що видав Його.
6 Da Yesu ya ce, “Ni ne shi,” sai suka ja da baya suka fāɗi a ƙasa.
I як тільки сказав їм: „Це Я“, вони подали́ся назад, та й на землю попа́дали.
7 Sai ya sāke tambayar su ya ce, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
І Він знов запитав їх: „Кого́ ви шукаєте?“Вони ж відказали: „Ісуса Назаряни́на“.
8 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku ni ne shi. In kuma ni ne kuke nema, to, sai ku bar waɗannan su tafi.”
Ісус відповів: „Я сказав вам, що це Я. Отож, як Мене ви шукаєте, то дайте оцим відійти “, —
9 Wannan ya faru ne don a cika kalmomin da ya yi cewa, “Ban yar da ko ɗaya daga cikin waɗanda ka ba ni ba.”
щоб збулося те слово, що Він був сказав: „Я не втратив ніко́го із тих, кого дав Ти Мені“.
10 Sai Siman Bitrus, wanda yake da takobi, ya zāre, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama (Sunan bawan kuwa Malkus ne.)
Тоді Си́мон Петро, меча мавши, його ви́хопив, і рубону́в раба́ первосвященика, — і відтя́в праве́ вухо йому́. А рабу́ на ім'я́ було Малх.
11 Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
Та промовив Ісус до Петра: Всунь у пі́хви меча! Чи ж не мав би Я пити ту чашу, що Отець дав Мені?“
12 Sai ƙungiyar soja tare da shugaban sojanta da kuma ma’aikatan Yahudawa suka kama Yesu. Suka daure shi
Відділ же війська та тисяцький і служба юдейська схопи́ли Ісуса, і зв'язали Його,
13 sa’an nan suka kawo shi da farko wurin Annas, wanda yake surukin Kayifas, babban firist a shekaran nan.
і повели Його перше до Анни, бо тестем доводивсь Кайяфі, що первосвящеником був того року.
14 Kayifas ne wanda ya shawarci Yahudawa cewa zai fi kyau mutum ɗaya yă mutu saboda mutane.
Це ж був той Кайя́фа, що порадив юдеям, що ліпше померти люди́ні одній за наро́д.
15 Siman Bitrus da kuma wani almajiri suna bin Yesu. Domin almajirin nan sananne ne ga babban firist, sai ya shiga tare da Yesu a filin gidan babban firist ɗin,
А Симон Петро й інший учень ішли за Ісусом слідо́м. Той же учень відо́мий був первосвященикові, і ввійшов у двір первосвящеників із Ісусом.
16 Bitrus kuwa ya dakata a waje a bakin ƙofa. Almajirin nan da yake sananne ga babban firist, ya dawo ya yi magana da yarinyar mai aiki a can, ya kuma shigo da Bitrus.
А Петро за ворітьми стояв. Тоді вийшов той учень, що відо́мий був первосвященикові, і сказав ворота́рці, — і впровадив Петра.
17 Yarinyar da take bakin ƙofar ta ce wa Bitrus, “Kai ba ɗaya ne daga cikin almajiran mutumin nan ba ne?” Bitrus ya amsa ya ce, “A’a, ba na ciki.”
І питає Петра ворота́рка служни́ця: „Ти хіба не з учнів Цього Чоловіка?“Той відказує: „Ні!“
18 To, ana sanyi, bayi da ma’aikatan suna tsattsaye kewaye da wutar da suka hura don su ji ɗumi. Bitrus ma yana tsaye tare da su, yana jin ɗumi.
А раби й служба, розклавши огонь, стояли та й грілися, бо був холод. І Петро стояв із ними та грівся.
19 Ana cikin haka, sai babban firist ya tuhumi Yesu game da almajiransa da kuma koyarwarsa.
А первосвященик спитався Ісуса про учнів Його, і про науку Його.
20 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a fili. Na kuma sha yin koyarwa a majami’u ko kuma a haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban taɓa faɗin kome a ɓoye ba.
Ісус Йому відповідь дав: „Я світові явно казав. Я постійно навчав у синагозі й у храмі, куди всі юдеї збираються, а таємно нічо́го Я не говорив.
21 Don me kake tuhumata? Ka tambayi waɗanda suka ji ni. Ba shakka, sun san abin da na faɗa.”
Чого ти питаєш Мене? Поспитайся тих, що чули, що́ Я їм говорив. Отже, знають вони, про що Я говорив“.
22 Da Yesu ya faɗa haka, sai ɗaya daga cikin ma’aikatan da yake tsaye kusa ya mare shi a fuska ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?”
А як Він це сказав, то один із присутньої там служби вдарив Ісуса в щоку́, говорячи: „То так відповідаєш первосвященикові?“
23 Yesu ya amsa ya ce, “In na faɗi abin da ba daidai ba, ka nuna abin da ba daidai ba. Amma in gaskiya na faɗa, don me ka mare ni?”
Ісус йому відповідь дав: „Якщо зле Я сказав, — покажи, що то зле; коли ж добре, — за що́ Мене б'єш?“
24 Sai Annas ya aika da shi, a daure, wurin Kayifas babban firist.
І відіслав Його Анна зв'язаним первосвященикові Кайяфі.
25 Da Siman Bitrus yana nan tsaye yana jin ɗumin wuta, sai aka tambaye shi, “Kai, kai ma ba ɗaya daga cikin almajiransa ba ne?” Sai ya yi mūsu, yana cewa, “Sam, ba na ciki.”
А Си́мон Петро стояв, гріючись. І сказали до нього: „Чи й ти не з учнів Його?“Він відрікся й сказав: „Ні!“
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist dangin wanda Bitrus ya sare wa kunne, ya tambaya shi ya ce, “Kana tsammani ban gan ka tare da shi a gonar zaitun ba?”
Говорить один із рабів первосвященика, родич тому́, що йому Петро вухо відтя́в: „Чи тебе я не бачив у саду́ з Ним?“
27 Bitrus ya sāke yin mūsu, nan take kuwa zakara ya yi cara.
І зно́ву відрікся Петро, — і заспівав півень хвилі тієї.
28 Sa’an nan Yahudawa suka fitar da Yesu daga wurin Kayifas zuwa fadar gwamnar Roma. A yanzu dai, safiya ta yi, don gudu kada su ƙazantar da kansu Yahudawa ba su shiga cikin fadar ba; sun so su iya ci Bikin Ƙetarewa.
А Ісуса ведуть від Кайяфи в прето́рій. Був же ра́нок. Та вони не ввійшли до прето́рія, щоб не опога́нитись, а щоб їсти пасху.
29 Saboda haka Bilatus ya fito wajensu ya ce, “Wace ƙara kuke kawowa game da mutumin nan?”
Тоді вийшов Пилат назо́вні до них і сказав: „Яку ска́ргу приносите ви на Цього Чоловіка?“
30 Suka amsa suka ce, “Da a ce shi ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bashe shi gare ka ba.”
Вони відповіли та й сказали йому: „Коли́ б Цей злочи́нцем не був, ми б Його тобі не видавали“.
31 Bilatus ya ce, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga dokarku.” Sai Yahudawa suka ƙi suka ce, “Ba mu da ikon yanke wa wani hukuncin kisa.”
А Пилат їм сказав: „Візьміть Його, та й за вашим Зако́ном судіть Його“. Юдеї сказали йому: „Нам не вільно нікого вбивати“, —
32 Wannan kuwa ya faru ne don a cika kalmomin da Yesu ya yi da suka nuna irin mutuwar da zai yi.
щоб збулося Ісусове слово, що його Він прорік, зазначаючи, якою то смертю Він має померти.
33 Sai Bilatus ya koma cikin fada, ya kira Yesu ya tambaye shi, “Shin, kai ne sarkin Yahudawa?”
Тоді зно́ву Пилат увійшов у прето́рій, і покликав Ісуса, і до Нього сказав: „Чи Ти Цар Юдейський?“
34 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Wannan ra’ayin kanka ne, ko waɗansu ne suka yi maka magana game da ni?”
Ісус відповів: „Чи від себе самого питаєш ти це, чи то інші тобі говорили про Мене?“
35 Bilatus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne? Ai, mutanenka ne da kuma manyan firistoci suka bashe ka gare ni. Me ka yi?”
Пилат відповів: „Чи ж юде́янин я? Твій наро́д та первосвященики мені Тебе видали. Що таке Ти вчинив?“
36 Yesu ya ce, “Mulkina ba na duniyan nan ba ne. Da na duniyan nan ne da bayina sun yi yaƙi su hana Yahudawa kama ni. Amma fa mulkina daga wani waje ne.”
Ісус відповів: „Моє Царство не із світу цього́. Якби із цього світу було́ Моє Царство, то служба Моя́ воювала б, щоб не ви́даний був Я юдеям. Та тепер Моє Царство не звідси“.
37 Sai Bilatus ya ce, “To, wato, kai sarki ne!” Yesu ya amsa ya ce, “Haka yake, ni sarki ne yadda ka faɗa. Tabbatacce, saboda wannan dalili ne aka haife ni, kuma don wannan ne na zo duniya, domin in shaidi gaskiya. Duk wanda yake gefen gaskiya yakan saurare ni.”
Сказав же до Нього Пила́т: „Так Ти Цар?“Ісус відповів: „Сам ти кажеш, що Цар Я. Я на те народився, і на те прийшов у світ, щоб засві́дчити правду. І кожен, хто з правди, той чує Мій голос“.
38 Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Mece ce gaskiya?” Da ya faɗi haka, sai ya sāke fitowa wurin Yahudawa ya ce, “Ni fa ban sami wani abin zargi game da shi ba.
Говорить до Нього Пила́т: „Що є правда?“І сказавши оце, до юдеїв знов вийшов, та й каже до них: „Не знахо́джу Я в Ньому провини нія́кої.
39 Amma fa kuna da wata al’ada in lokacin Bikin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku da ɗan kurkuku ɗaya. To, kuna so in sakar muku ‘sarkin Yahudawa’?”
Та ви маєте зви́чай, щоб я випустив вам одно́го на Пасху. Чи хочете отже, — відпущу́ вам Царя Юдейського?“
40 Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “Kai, ba shi ba! A ba mu Barabbas!” To, Barabbas ɗin nan yana da hannu dumu-dumu a wani tawaye.
Та зно́ву вони зняли крик, вимагаючи: „Не Його, а Вара́вву!“А Вара́вва був злочи́нець.