< Yohanna 18 >

1 Da ya gama addu’a, sai Yesu ya fita tare da almajiransa suka haye Kwarin Kidron. A wancan ƙetaren kuwa akwai lambun zaitun, da shi da almajiransa suka shiga ciki.
tAH kathAH kathayitvA yIzuH ziSyAnAdAya kidronnAmakaM srota uttIryya ziSyaiH saha tatratyodyAnaM prAvizat|
2 To, Yahuda, wanda ya bashe shi, ya san wurin, domin Yesu ya sha zuwa wurin da almajiransa.
kintu vizvAsaghAtiyihUdAstat sthAnaM paricIyate yato yIzuH ziSyaiH sArddhaM kadAcit tat sthAnam agacchat|
3 Saboda haka Yahuda ya zo cikin lambun, yana jagoranta ƙungiyar sojoji da waɗansu ma’aikata daga wurin manyan firistoci da Farisiyawa. Suna riƙe da toci, fitilu da kuma makamai.
tadA sa yihUdAH sainyagaNaM pradhAnayAjakAnAM phirUzinAJca padAtigaNaJca gRhItvA pradIpAn ulkAn astrANi cAdAya tasmin sthAna upasthitavAn|
4 Yesu kuwa, sane da duk abin da zai same shi, ya fito ya tambaye, su ya ce, “Wa kuke nema?”
svaM prati yad ghaTiSyate taj jJAtvA yIzuragresaraH san tAnapRcchat kaM gaveSayatha?
5 Suka amsa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce, “Ni ne shi.” (Yahuda kuwa wanda ya bashe shi yana nan tsaye tare da su.)
te pratyavadan, nAsaratIyaM yIzuM; tato yIzuravAdId ahameva saH; taiH saha vizvAsaghAtI yihUdAzcAtiSThat|
6 Da Yesu ya ce, “Ni ne shi,” sai suka ja da baya suka fāɗi a ƙasa.
tadAhameva sa tasyaitAM kathAM zrutvaiva te pazcAdetya bhUmau patitAH|
7 Sai ya sāke tambayar su ya ce, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
tato yIzuH punarapi pRSThavAn kaM gaveSayatha? tataste pratyavadan nAsaratIyaM yIzuM|
8 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku ni ne shi. In kuma ni ne kuke nema, to, sai ku bar waɗannan su tafi.”
tadA yIzuH pratyuditavAn ahameva sa imAM kathAmacakatham; yadi mAmanvicchatha tarhImAn gantuM mA vArayata|
9 Wannan ya faru ne don a cika kalmomin da ya yi cewa, “Ban yar da ko ɗaya daga cikin waɗanda ka ba ni ba.”
itthaM bhUte mahyaM yAllokAn adadAsteSAm ekamapi nAhArayam imAM yAM kathAM sa svayamakathayat sA kathA saphalA jAtA|
10 Sai Siman Bitrus, wanda yake da takobi, ya zāre, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama (Sunan bawan kuwa Malkus ne.)
tadA zimonpitarasya nikaTe khaGgalsthiteH sa taM niSkoSaM kRtvA mahAyAjakasya mAlkhanAmAnaM dAsam Ahatya tasya dakSiNakarNaM chinnavAn|
11 Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
tato yIzuH pitaram avadat, khaGgaM koSe sthApaya mama pitA mahyaM pAtuM yaM kaMsam adadAt tenAhaM kiM na pAsyAmi?
12 Sai ƙungiyar soja tare da shugaban sojanta da kuma ma’aikatan Yahudawa suka kama Yesu. Suka daure shi
tadA sainyagaNaH senApati ryihUdIyAnAM padAtayazca yIzuM ghRtvA baddhvA hAnannAmnaH kiyaphAH zvazurasya samIpaM prathamam anayan|
13 sa’an nan suka kawo shi da farko wurin Annas, wanda yake surukin Kayifas, babban firist a shekaran nan.
sa kiyaphAstasmin vatsare mahAyAjatvapade niyuktaH
14 Kayifas ne wanda ya shawarci Yahudawa cewa zai fi kyau mutum ɗaya yă mutu saboda mutane.
san sAdhAraNalokAnAM maGgalArtham ekajanasya maraNamucitam iti yihUdIyaiH sArddham amantrayat|
15 Siman Bitrus da kuma wani almajiri suna bin Yesu. Domin almajirin nan sananne ne ga babban firist, sai ya shiga tare da Yesu a filin gidan babban firist ɗin,
tadA zimonpitaro'nyaikaziSyazca yIzoH pazcAd agacchatAM tasyAnyaziSyasya mahAyAjakena paricitatvAt sa yIzunA saha mahAyAjakasyATTAlikAM prAvizat|
16 Bitrus kuwa ya dakata a waje a bakin ƙofa. Almajirin nan da yake sananne ga babban firist, ya dawo ya yi magana da yarinyar mai aiki a can, ya kuma shigo da Bitrus.
kintu pitaro bahirdvArasya samIpe'tiSThad ataeva mahAyAjakena paricitaH sa ziSyaH punarbahirgatvA dauvAyikAyai kathayitvA pitaram abhyantaram Anayat|
17 Yarinyar da take bakin ƙofar ta ce wa Bitrus, “Kai ba ɗaya ne daga cikin almajiran mutumin nan ba ne?” Bitrus ya amsa ya ce, “A’a, ba na ciki.”
tadA sa dvArarakSikA pitaram avadat tvaM kiM na tasya mAnavasya ziSyaH? tataH sovadad ahaM na bhavAmi|
18 To, ana sanyi, bayi da ma’aikatan suna tsattsaye kewaye da wutar da suka hura don su ji ɗumi. Bitrus ma yana tsaye tare da su, yana jin ɗumi.
tataH paraM yatsthAne dAsAH padAtayazca zItahetoraGgArai rvahniM prajvAlya tApaM sevitavantastatsthAne pitarastiSThan taiH saha vahnitApaM sevitum Arabhata|
19 Ana cikin haka, sai babban firist ya tuhumi Yesu game da almajiransa da kuma koyarwarsa.
tadA ziSyeSUpadeze ca mahAyAjakena yIzuH pRSTaH
20 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a fili. Na kuma sha yin koyarwa a majami’u ko kuma a haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban taɓa faɗin kome a ɓoye ba.
san pratyuktavAn sarvvalokAnAM samakSaM kathAmakathayaM guptaM kAmapi kathAM na kathayitvA yat sthAnaM yihUdIyAH satataM gacchanti tatra bhajanagehe mandire cAzikSayaM|
21 Don me kake tuhumata? Ka tambayi waɗanda suka ji ni. Ba shakka, sun san abin da na faɗa.”
mattaH kutaH pRcchasi? ye janA madupadezam azRNvan tAneva pRccha yadyad avadaM te tat jAninta|
22 Da Yesu ya faɗa haka, sai ɗaya daga cikin ma’aikatan da yake tsaye kusa ya mare shi a fuska ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?”
tadetthaM pratyuditatvAt nikaTasthapadAti ryIzuM capeTenAhatya vyAharat mahAyAjakam evaM prativadasi?
23 Yesu ya amsa ya ce, “In na faɗi abin da ba daidai ba, ka nuna abin da ba daidai ba. Amma in gaskiya na faɗa, don me ka mare ni?”
tato yIzuH pratigaditavAn yadyayathArtham acakathaM tarhi tasyAyathArthasya pramANaM dehi, kintu yadi yathArthaM tarhi kuto heto rmAm atADayaH?
24 Sai Annas ya aika da shi, a daure, wurin Kayifas babban firist.
pUrvvaM hAnan sabandhanaM taM kiyaphAmahAyAjakasya samIpaM praiSayat|
25 Da Siman Bitrus yana nan tsaye yana jin ɗumin wuta, sai aka tambaye shi, “Kai, kai ma ba ɗaya daga cikin almajiransa ba ne?” Sai ya yi mūsu, yana cewa, “Sam, ba na ciki.”
zimonpitarastiSThan vahnitApaM sevate, etasmin samaye kiyantastam apRcchan tvaM kim etasya janasya ziSyo na? tataH sopahnutyAbravId ahaM na bhavAmi|
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist dangin wanda Bitrus ya sare wa kunne, ya tambaya shi ya ce, “Kana tsammani ban gan ka tare da shi a gonar zaitun ba?”
tadA mahAyAjakasya yasya dAsasya pitaraH karNamacchinat tasya kuTumbaH pratyuditavAn udyAne tena saha tiSThantaM tvAM kiM nApazyaM?
27 Bitrus ya sāke yin mūsu, nan take kuwa zakara ya yi cara.
kintu pitaraH punarapahnutya kathitavAn; tadAnIM kukkuTo'raut|
28 Sa’an nan Yahudawa suka fitar da Yesu daga wurin Kayifas zuwa fadar gwamnar Roma. A yanzu dai, safiya ta yi, don gudu kada su ƙazantar da kansu Yahudawa ba su shiga cikin fadar ba; sun so su iya ci Bikin Ƙetarewa.
tadanantaraM pratyUSe te kiyaphAgRhAd adhipate rgRhaM yIzum anayan kintu yasmin azucitve jAte tai rnistArotsave na bhoktavyaM, tasya bhayAd yihUdIyAstadgRhaM nAvizan|
29 Saboda haka Bilatus ya fito wajensu ya ce, “Wace ƙara kuke kawowa game da mutumin nan?”
aparaM pIlAto bahirAgatya tAn pRSThavAn etasya manuSyasya kaM doSaM vadatha?
30 Suka amsa suka ce, “Da a ce shi ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bashe shi gare ka ba.”
tadA te petyavadan duSkarmmakAriNi na sati bhavataH samIpe nainaM samArpayiSyAmaH|
31 Bilatus ya ce, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga dokarku.” Sai Yahudawa suka ƙi suka ce, “Ba mu da ikon yanke wa wani hukuncin kisa.”
tataH pIlAto'vadad yUyamenaM gRhItvA sveSAM vyavasthayA vicArayata| tadA yihUdIyAH pratyavadan kasyApi manuSyasya prANadaNDaM karttuM nAsmAkam adhikAro'sti|
32 Wannan kuwa ya faru ne don a cika kalmomin da Yesu ya yi da suka nuna irin mutuwar da zai yi.
evaM sati yIzuH svasya mRtyau yAM kathAM kathitavAn sA saphalAbhavat|
33 Sai Bilatus ya koma cikin fada, ya kira Yesu ya tambaye shi, “Shin, kai ne sarkin Yahudawa?”
tadanantaraM pIlAtaH punarapi tad rAjagRhaM gatvA yIzumAhUya pRSTavAn tvaM kiM yihUdIyAnAM rAjA?
34 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Wannan ra’ayin kanka ne, ko waɗansu ne suka yi maka magana game da ni?”
yIzuH pratyavadat tvam etAM kathAM svataH kathayasi kimanyaH kazcin mayi kathitavAn?
35 Bilatus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne? Ai, mutanenka ne da kuma manyan firistoci suka bashe ka gare ni. Me ka yi?”
pIlAto'vadad ahaM kiM yihUdIyaH? tava svadezIyA vizeSataH pradhAnayAjakA mama nikaTe tvAM samArpayana, tvaM kiM kRtavAn?
36 Yesu ya ce, “Mulkina ba na duniyan nan ba ne. Da na duniyan nan ne da bayina sun yi yaƙi su hana Yahudawa kama ni. Amma fa mulkina daga wani waje ne.”
yIzuH pratyavadat mama rAjyam etajjagatsambandhIyaM na bhavati yadi mama rAjyaM jagatsambandhIyam abhaviSyat tarhi yihUdIyAnAM hasteSu yathA samarpito nAbhavaM tadarthaM mama sevakA ayotsyan kintu mama rAjyam aihikaM na|
37 Sai Bilatus ya ce, “To, wato, kai sarki ne!” Yesu ya amsa ya ce, “Haka yake, ni sarki ne yadda ka faɗa. Tabbatacce, saboda wannan dalili ne aka haife ni, kuma don wannan ne na zo duniya, domin in shaidi gaskiya. Duk wanda yake gefen gaskiya yakan saurare ni.”
tadA pIlAtaH kathitavAn, tarhi tvaM rAjA bhavasi? yIzuH pratyuktavAn tvaM satyaM kathayasi, rAjAhaM bhavAmi; satyatAyAM sAkSyaM dAtuM janiM gRhItvA jagatyasmin avatIrNavAn, tasmAt satyadharmmapakSapAtino mama kathAM zRNvanti|
38 Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Mece ce gaskiya?” Da ya faɗi haka, sai ya sāke fitowa wurin Yahudawa ya ce, “Ni fa ban sami wani abin zargi game da shi ba.
tadA satyaM kiM? etAM kathAM paSTvA pIlAtaH punarapi bahirgatvA yihUdIyAn abhASata, ahaM tasya kamapyaparAdhaM na prApnomi|
39 Amma fa kuna da wata al’ada in lokacin Bikin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku da ɗan kurkuku ɗaya. To, kuna so in sakar muku ‘sarkin Yahudawa’?”
nistArotsavasamaye yuSmAbhirabhirucita eko jano mayA mocayitavya eSA yuSmAkaM rItirasti, ataeva yuSmAkaM nikaTe yihUdIyAnAM rAjAnaM kiM mocayAmi, yuSmAkam icchA kA?
40 Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “Kai, ba shi ba! A ba mu Barabbas!” To, Barabbas ɗin nan yana da hannu dumu-dumu a wani tawaye.
tadA te sarvve ruvanto vyAharan enaM mAnuSaM nahi barabbAM mocaya| kintu sa barabbA dasyurAsIt|

< Yohanna 18 >