< Yohanna 18 >

1 Da ya gama addu’a, sai Yesu ya fita tare da almajiransa suka haye Kwarin Kidron. A wancan ƙetaren kuwa akwai lambun zaitun, da shi da almajiransa suka shiga ciki.
Après avoir prononcé ces paroles, Jésus sortit avec ses disciples de l'autre côté du torrent de Cédron, où il y avait un jardin, dans lequel il entra avec ses disciples.
2 To, Yahuda, wanda ya bashe shi, ya san wurin, domin Yesu ya sha zuwa wurin da almajiransa.
Judas, qui le trahissait, connaissait aussi ce lieu, car Jésus s'y réunissait souvent avec ses disciples.
3 Saboda haka Yahuda ya zo cikin lambun, yana jagoranta ƙungiyar sojoji da waɗansu ma’aikata daga wurin manyan firistoci da Farisiyawa. Suna riƙe da toci, fitilu da kuma makamai.
Judas donc, ayant pris un détachement de soldats et d'officiers des principaux sacrificateurs et des pharisiens, y vint avec des lanternes, des torches et des armes.
4 Yesu kuwa, sane da duk abin da zai same shi, ya fito ya tambaye, su ya ce, “Wa kuke nema?”
Jésus donc, sachant tout ce qui lui arrivait, sortit et leur dit: « Qui cherchez-vous? »
5 Suka amsa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce, “Ni ne shi.” (Yahuda kuwa wanda ya bashe shi yana nan tsaye tare da su.)
Ils lui répondirent: « Jésus de Nazareth. » Jésus leur dit: « Je suis lui. » Judas, qui le livrait, se tenait aussi avec eux.
6 Da Yesu ya ce, “Ni ne shi,” sai suka ja da baya suka fāɗi a ƙasa.
Lorsqu'il leur dit: « C'est moi », ils reculèrent et tombèrent à terre.
7 Sai ya sāke tambayar su ya ce, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
Il leur demanda donc à nouveau: « Qui cherchez-vous? » Ils ont dit: « Jésus de Nazareth. »
8 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku ni ne shi. In kuma ni ne kuke nema, to, sai ku bar waɗannan su tafi.”
Jésus répondit: « Je vous ai dit que c'était moi. Si donc vous me cherchez, laissez ceux-là s'en aller, »
9 Wannan ya faru ne don a cika kalmomin da ya yi cewa, “Ban yar da ko ɗaya daga cikin waɗanda ka ba ni ba.”
afin que s'accomplisse la parole qu'il a dite: « De ceux que tu m'as donnés, je n'ai perdu aucun. »
10 Sai Siman Bitrus, wanda yake da takobi, ya zāre, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama (Sunan bawan kuwa Malkus ne.)
Simon-Pierre, ayant une épée, la tira, frappa le serviteur du souverain sacrificateur, et lui coupa l'oreille droite. Le nom du serviteur était Malchus.
11 Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
Jésus dit alors à Pierre: « Remets l'épée dans son fourreau. La coupe que le Père m'a donnée, ne la boirai-je pas? »
12 Sai ƙungiyar soja tare da shugaban sojanta da kuma ma’aikatan Yahudawa suka kama Yesu. Suka daure shi
Le détachement, le commandant et les officiers des Juifs se saisirent donc de Jésus, le lièrent,
13 sa’an nan suka kawo shi da farko wurin Annas, wanda yake surukin Kayifas, babban firist a shekaran nan.
et le conduisirent d'abord chez Anne, car il était beau-père de Caïphe, qui était grand prêtre cette année-là.
14 Kayifas ne wanda ya shawarci Yahudawa cewa zai fi kyau mutum ɗaya yă mutu saboda mutane.
Or, c'est Caïphe qui avait conseillé aux Juifs qu'il convenait qu'un seul homme périsse pour le peuple.
15 Siman Bitrus da kuma wani almajiri suna bin Yesu. Domin almajirin nan sananne ne ga babban firist, sai ya shiga tare da Yesu a filin gidan babban firist ɗin,
Simon Pierre suivait Jésus, ainsi qu'un autre disciple. Or ce disciple était connu du grand prêtre, et il entra avec Jésus dans la cour du grand prêtre;
16 Bitrus kuwa ya dakata a waje a bakin ƙofa. Almajirin nan da yake sananne ga babban firist, ya dawo ya yi magana da yarinyar mai aiki a can, ya kuma shigo da Bitrus.
mais Pierre se tenait à la porte, dehors. L'autre disciple, qui était connu du grand prêtre, sortit donc, parla à la servante qui gardait la porte, et fit entrer Pierre.
17 Yarinyar da take bakin ƙofar ta ce wa Bitrus, “Kai ba ɗaya ne daga cikin almajiran mutumin nan ba ne?” Bitrus ya amsa ya ce, “A’a, ba na ciki.”
Alors la servante qui gardait la porte dit à Pierre: « Es-tu aussi un des disciples de cet homme? » Il a dit: « Je ne le suis pas. »
18 To, ana sanyi, bayi da ma’aikatan suna tsattsaye kewaye da wutar da suka hura don su ji ɗumi. Bitrus ma yana tsaye tare da su, yana jin ɗumi.
Or les serviteurs et les officiers se tenaient là, ayant fait un feu de charbons, car il faisait froid. Ils se chauffaient. Pierre était avec eux, debout et se réchauffant.
19 Ana cikin haka, sai babban firist ya tuhumi Yesu game da almajiransa da kuma koyarwarsa.
Le grand prêtre interrogea donc Jésus sur ses disciples et sur son enseignement.
20 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a fili. Na kuma sha yin koyarwa a majami’u ko kuma a haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban taɓa faɗin kome a ɓoye ba.
Jésus lui répondit: « J'ai parlé ouvertement au monde. J'ai toujours enseigné dans les synagogues et dans le temple, là où les Juifs se réunissent toujours. Je n'ai rien dit en secret.
21 Don me kake tuhumata? Ka tambayi waɗanda suka ji ni. Ba shakka, sun san abin da na faɗa.”
Pourquoi m'interroges-tu? Demandez à ceux qui m'ont entendu ce que je leur ai dit. Voici, ils savent les choses que j'ai dites. »
22 Da Yesu ya faɗa haka, sai ɗaya daga cikin ma’aikatan da yake tsaye kusa ya mare shi a fuska ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?”
Lorsqu'il eut dit cela, l'un des officiers qui se tenait là frappa Jésus de la main, en disant: « C'est ainsi que tu réponds au grand prêtre? »
23 Yesu ya amsa ya ce, “In na faɗi abin da ba daidai ba, ka nuna abin da ba daidai ba. Amma in gaskiya na faɗa, don me ka mare ni?”
Jésus lui répondit: « Si j'ai mal parlé, témoigne du mal; mais si j'ai bien parlé, pourquoi me frappes-tu? »
24 Sai Annas ya aika da shi, a daure, wurin Kayifas babban firist.
Annas l'envoya lié à Caïphe, le grand prêtre.
25 Da Siman Bitrus yana nan tsaye yana jin ɗumin wuta, sai aka tambaye shi, “Kai, kai ma ba ɗaya daga cikin almajiransa ba ne?” Sai ya yi mūsu, yana cewa, “Sam, ba na ciki.”
Or Simon-Pierre était debout et se chauffait. Ils lui dirent donc: « Tu n'es pas aussi un de ses disciples, n'est-ce pas? » Il l'a nié et a dit: « Je ne le suis pas. »
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist dangin wanda Bitrus ya sare wa kunne, ya tambaya shi ya ce, “Kana tsammani ban gan ka tare da shi a gonar zaitun ba?”
Un des serviteurs du grand prêtre, parent de celui à qui Pierre avait coupé l'oreille, dit: « Ne t'ai-je pas vu avec lui dans le jardin? »
27 Bitrus ya sāke yin mūsu, nan take kuwa zakara ya yi cara.
Pierre le renia donc de nouveau, et aussitôt le coq chanta.
28 Sa’an nan Yahudawa suka fitar da Yesu daga wurin Kayifas zuwa fadar gwamnar Roma. A yanzu dai, safiya ta yi, don gudu kada su ƙazantar da kansu Yahudawa ba su shiga cikin fadar ba; sun so su iya ci Bikin Ƙetarewa.
Ils conduisirent donc Jésus de chez Caïphe au prétoire. C'était de bonne heure, et eux-mêmes n'entraient pas dans le prétoire, afin de ne pas se souiller, mais de pouvoir manger la Pâque.
29 Saboda haka Bilatus ya fito wajensu ya ce, “Wace ƙara kuke kawowa game da mutumin nan?”
Pilate sortit donc vers eux et dit: « Quelle accusation portez-vous contre cet homme? »
30 Suka amsa suka ce, “Da a ce shi ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bashe shi gare ka ba.”
Ils lui répondirent: « Si cet homme n'était pas un malfaiteur, nous ne te l'aurions pas livré. »
31 Bilatus ya ce, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga dokarku.” Sai Yahudawa suka ƙi suka ce, “Ba mu da ikon yanke wa wani hukuncin kisa.”
Pilate leur dit donc: « Prenez-le vous-mêmes, et jugez-le selon votre loi. » C'est pourquoi les Juifs lui dirent: « Il nous est interdit de mettre quelqu'un à mort »,
32 Wannan kuwa ya faru ne don a cika kalmomin da Yesu ya yi da suka nuna irin mutuwar da zai yi.
afin que s'accomplisse la parole de Jésus, qu'il avait prononcée, en indiquant par quel genre de mort il devait mourir.
33 Sai Bilatus ya koma cikin fada, ya kira Yesu ya tambaye shi, “Shin, kai ne sarkin Yahudawa?”
Pilate entra donc de nouveau dans le prétoire, appela Jésus, et lui dit: « Es-tu le roi des Juifs? »
34 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Wannan ra’ayin kanka ne, ko waɗansu ne suka yi maka magana game da ni?”
Jésus lui répondit: « Tu dis cela tout seul, ou bien d'autres t'ont-ils parlé de moi? »
35 Bilatus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne? Ai, mutanenka ne da kuma manyan firistoci suka bashe ka gare ni. Me ka yi?”
Pilate répondit: « Je ne suis pas Juif, n'est-ce pas? Ta propre nation et les chefs des prêtres t'ont livré à moi. Qu'as-tu fait? »
36 Yesu ya ce, “Mulkina ba na duniyan nan ba ne. Da na duniyan nan ne da bayina sun yi yaƙi su hana Yahudawa kama ni. Amma fa mulkina daga wani waje ne.”
Jésus répondit: « Mon Royaume n'est pas de ce monde. Si mon Royaume était de ce monde, alors mes serviteurs combattraient, pour que je ne sois pas livré aux Juifs. Mais maintenant, mon Royaume n'est pas d'ici-bas. »
37 Sai Bilatus ya ce, “To, wato, kai sarki ne!” Yesu ya amsa ya ce, “Haka yake, ni sarki ne yadda ka faɗa. Tabbatacce, saboda wannan dalili ne aka haife ni, kuma don wannan ne na zo duniya, domin in shaidi gaskiya. Duk wanda yake gefen gaskiya yakan saurare ni.”
Pilate lui dit donc: « Es-tu donc un roi? » Jésus répondit: « Vous dites que je suis un roi. C'est pour cela que je suis né, et c'est pour cela que je suis venu dans le monde, afin de rendre témoignage à la vérité. Tous ceux qui sont de la vérité écoutent ma voix. »
38 Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Mece ce gaskiya?” Da ya faɗi haka, sai ya sāke fitowa wurin Yahudawa ya ce, “Ni fa ban sami wani abin zargi game da shi ba.
Pilate lui dit: « Qu'est-ce que la vérité? » Après avoir dit cela, il sortit de nouveau vers les Juifs, et leur dit: « Je ne trouve aucun motif d'accusation contre lui.
39 Amma fa kuna da wata al’ada in lokacin Bikin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku da ɗan kurkuku ɗaya. To, kuna so in sakar muku ‘sarkin Yahudawa’?”
Mais vous avez pour coutume que je vous livre quelqu'un à la Pâque. Voulez-vous donc que je vous relâche le roi des Juifs? »
40 Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “Kai, ba shi ba! A ba mu Barabbas!” To, Barabbas ɗin nan yana da hannu dumu-dumu a wani tawaye.
Alors ils crièrent tous à nouveau, disant: « Pas cet homme, mais Barabbas! » Or Barabbas était un brigand.

< Yohanna 18 >