< Yohanna 18 >
1 Da ya gama addu’a, sai Yesu ya fita tare da almajiransa suka haye Kwarin Kidron. A wancan ƙetaren kuwa akwai lambun zaitun, da shi da almajiransa suka shiga ciki.
Having said these things, Jesus, went out, with his disciples, across the winter-torrent of the Kedron, where was a garden, —into which he entered, he, and his disciples.
2 To, Yahuda, wanda ya bashe shi, ya san wurin, domin Yesu ya sha zuwa wurin da almajiransa.
Now, Judas also, who was delivering him up, knew the place: because, oft, had Jesus been gathered there, with his disciples.
3 Saboda haka Yahuda ya zo cikin lambun, yana jagoranta ƙungiyar sojoji da waɗansu ma’aikata daga wurin manyan firistoci da Farisiyawa. Suna riƙe da toci, fitilu da kuma makamai.
Judas, therefore, receiving the band, and officers, from among the High-priests and [from among] the Pharisees, cometh thither, with lights and torches and weapons.
4 Yesu kuwa, sane da duk abin da zai same shi, ya fito ya tambaye, su ya ce, “Wa kuke nema?”
Jesus, therefore, knowing all the things coming upon him, went forth, and saith unto them—Whom, seek ye?
5 Suka amsa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce, “Ni ne shi.” (Yahuda kuwa wanda ya bashe shi yana nan tsaye tare da su.)
They answered him—Jesus, the Nazarene. He saith unto them—I, am he. Now Judas also, who was delivering him up, was standing with them.
6 Da Yesu ya ce, “Ni ne shi,” sai suka ja da baya suka fāɗi a ƙasa.
When, therefore, he said unto them, I, am he, they went backwards, and fell to the ground.
7 Sai ya sāke tambayar su ya ce, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
Again, therefore, he questioned them—Whom, seek ye? And, they, said—Jesus, the Nazarene.
8 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku ni ne shi. In kuma ni ne kuke nema, to, sai ku bar waɗannan su tafi.”
Jesus answered—I told you, I, am he. If, then, ye seek me, let these go their way: —
9 Wannan ya faru ne don a cika kalmomin da ya yi cewa, “Ban yar da ko ɗaya daga cikin waɗanda ka ba ni ba.”
that the word might be fulfilled which he had said—As touching them whom thou hast given me, I lost from among them, not so much as one.
10 Sai Siman Bitrus, wanda yake da takobi, ya zāre, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama (Sunan bawan kuwa Malkus ne.)
Simon Peter, therefore, having a sword, drew it, and smote the High-priest’s servant, and cut off his right ear. Now the name of the servant was Malchus.
11 Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
Jesus, therefore, said unto Peter—Thrust the sword into its sheath: —The cup which the Father hath given me, shall I in anywise not drink it?
12 Sai ƙungiyar soja tare da shugaban sojanta da kuma ma’aikatan Yahudawa suka kama Yesu. Suka daure shi
The band, therefore, and the captain, and the officers of the Jews, apprehended Jesus, and bound him,
13 sa’an nan suka kawo shi da farko wurin Annas, wanda yake surukin Kayifas, babban firist a shekaran nan.
and led him unto Annas, first; for he was father-in-law of Caiaphas, who was the High-priest of that year.
14 Kayifas ne wanda ya shawarci Yahudawa cewa zai fi kyau mutum ɗaya yă mutu saboda mutane.
Now Caiaphas was he that gave counsel unto the Jews, that it was profitable for, one man, to die in behalf of the people.
15 Siman Bitrus da kuma wani almajiri suna bin Yesu. Domin almajirin nan sananne ne ga babban firist, sai ya shiga tare da Yesu a filin gidan babban firist ɗin,
And Simon Peter was following with Jesus, also another disciple. But, that disciple, was known unto the High-priest, and entered in, with Jesus, into the court of the High-priest;
16 Bitrus kuwa ya dakata a waje a bakin ƙofa. Almajirin nan da yake sananne ga babban firist, ya dawo ya yi magana da yarinyar mai aiki a can, ya kuma shigo da Bitrus.
whereas, Peter, remained standing at the door outside. The other disciple, therefore, that was known of the High-priest, went out, and spake unto the portress, and brought in Peter.
17 Yarinyar da take bakin ƙofar ta ce wa Bitrus, “Kai ba ɗaya ne daga cikin almajiran mutumin nan ba ne?” Bitrus ya amsa ya ce, “A’a, ba na ciki.”
The female servant, therefore, the portress, saith unto Peter—Art, thou also, from among the disciples of this man? He, saith—I am not!
18 To, ana sanyi, bayi da ma’aikatan suna tsattsaye kewaye da wutar da suka hura don su ji ɗumi. Bitrus ma yana tsaye tare da su, yana jin ɗumi.
Now the servants and the officers were standing by, having made, a coal fire, because it was cold, —and were warming themselves; and Peter also was with them, standing and warming himself.
19 Ana cikin haka, sai babban firist ya tuhumi Yesu game da almajiransa da kuma koyarwarsa.
The High-priest, therefore, questioned Jesus concerning his disciples, and concerning his teaching.
20 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a fili. Na kuma sha yin koyarwa a majami’u ko kuma a haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban taɓa faɗin kome a ɓoye ba.
Jesus answered him—I, openly, have spoken, unto the world, —I, ever, taught, in synagogue, and in the temple, where all the Jews gather together; and, in secret, spake nothing:
21 Don me kake tuhumata? Ka tambayi waɗanda suka ji ni. Ba shakka, sun san abin da na faɗa.”
Why questionest thou me? question them who have heard, what I spake unto them. See! these, know what, I, said.
22 Da Yesu ya faɗa haka, sai ɗaya daga cikin ma’aikatan da yake tsaye kusa ya mare shi a fuska ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?”
And, when, these things, he had said, one of the officers who was standing by, gave a smart blow to Jesus, saying—Thus, answerest thou, the High-priest?
23 Yesu ya amsa ya ce, “In na faɗi abin da ba daidai ba, ka nuna abin da ba daidai ba. Amma in gaskiya na faɗa, don me ka mare ni?”
Jesus answered him—If, with abuse, I spake, bear witness of the abuse: but, if with respect, why, smitest thou me?
24 Sai Annas ya aika da shi, a daure, wurin Kayifas babban firist.
Annas therefore sent him forth, bound, unto Caiaphas the High-priest.
25 Da Siman Bitrus yana nan tsaye yana jin ɗumin wuta, sai aka tambaye shi, “Kai, kai ma ba ɗaya daga cikin almajiransa ba ne?” Sai ya yi mūsu, yana cewa, “Sam, ba na ciki.”
Now Simon Peter was standing and warming himself. They said, therefore, unto him—Art, thou also, from among his disciples? He, denied, and said—I am not!
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist dangin wanda Bitrus ya sare wa kunne, ya tambaya shi ya ce, “Kana tsammani ban gan ka tare da shi a gonar zaitun ba?”
Saith one from among the servants of the High-priest, being, kinsman, of him whose ear Peter cut off, —Did not, I, see thee, in the garden with him?
27 Bitrus ya sāke yin mūsu, nan take kuwa zakara ya yi cara.
Again, therefore, Peter denied. And, straightway, a cock crew.
28 Sa’an nan Yahudawa suka fitar da Yesu daga wurin Kayifas zuwa fadar gwamnar Roma. A yanzu dai, safiya ta yi, don gudu kada su ƙazantar da kansu Yahudawa ba su shiga cikin fadar ba; sun so su iya ci Bikin Ƙetarewa.
So they lead Jesus from Caiaphas unto the judgment-hall. Now it was early; and, they themselves, entered not into the judgment-hall, that they might not be defiled, but might eat the passover.
29 Saboda haka Bilatus ya fito wajensu ya ce, “Wace ƙara kuke kawowa game da mutumin nan?”
Pilate, therefore, went forth outside unto them, and saith, —What accusation bring ye against this man?
30 Suka amsa suka ce, “Da a ce shi ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bashe shi gare ka ba.”
They answered and said unto him—If this one had not been doing, mischief, unto thee, had we not delivered him up.
31 Bilatus ya ce, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga dokarku.” Sai Yahudawa suka ƙi suka ce, “Ba mu da ikon yanke wa wani hukuncin kisa.”
Pilate, therefore, said unto them—Ye, take him, and, according to your law, judge ye him. The Jews said unto him—Unto us, it is not allowed, to kill anyone!—
32 Wannan kuwa ya faru ne don a cika kalmomin da Yesu ya yi da suka nuna irin mutuwar da zai yi.
that, the word of Jesus, might be fulfilled, which he spake, signifying, by what manner of death, he was about to die.
33 Sai Bilatus ya koma cikin fada, ya kira Yesu ya tambaye shi, “Shin, kai ne sarkin Yahudawa?”
Pilate, therefore, entered again into the judgment-hall; and addressed Jesus, and said unto him—Art, thou, the king of the Jews?
34 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Wannan ra’ayin kanka ne, ko waɗansu ne suka yi maka magana game da ni?”
Jesus answered—Of thyself, art, thou, this thing saying; or did, others, tell thee concerning me?
35 Bilatus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne? Ai, mutanenka ne da kuma manyan firistoci suka bashe ka gare ni. Me ka yi?”
Pilate answered—Am, I, a Jew? Thine own nation, and the High-priests, delivered thee up, unto me! What, hast thou done?
36 Yesu ya ce, “Mulkina ba na duniyan nan ba ne. Da na duniyan nan ne da bayina sun yi yaƙi su hana Yahudawa kama ni. Amma fa mulkina daga wani waje ne.”
Jesus answered—My kingdom, is not of this world: If, of this world, had been my kingdom, mine own officers, would have been striving, that I should not be delivered up unto the Jews: but, now, my kingdom, is not from hence.
37 Sai Bilatus ya ce, “To, wato, kai sarki ne!” Yesu ya amsa ya ce, “Haka yake, ni sarki ne yadda ka faɗa. Tabbatacce, saboda wannan dalili ne aka haife ni, kuma don wannan ne na zo duniya, domin in shaidi gaskiya. Duk wanda yake gefen gaskiya yakan saurare ni.”
Pilate, therefore, said unto him—And yet, thou, art, not a king? Jesus answered—Thou, sayest, that, a king, I am: I, for this, have been born, and, for this, have come into the world, —that I may bear witness unto the truth: Every one who is of the truth, hearkeneth unto my voice.
38 Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Mece ce gaskiya?” Da ya faɗi haka, sai ya sāke fitowa wurin Yahudawa ya ce, “Ni fa ban sami wani abin zargi game da shi ba.
Pilate saith unto him—What, is truth? And, this saying, again, went he out to the Jews, and saith unto them, —I, find in him, not a single fault.
39 Amma fa kuna da wata al’ada in lokacin Bikin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku da ɗan kurkuku ɗaya. To, kuna so in sakar muku ‘sarkin Yahudawa’?”
Howbeit ye have, a custom, that, some one, I should release unto you, during the passover: —Are ye minded, then, that I release unto you the king of the Jews?
40 Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “Kai, ba shi ba! A ba mu Barabbas!” To, Barabbas ɗin nan yana da hannu dumu-dumu a wani tawaye.
So they cried aloud again, saying—Not this man, but Barabbas! Now, Barabbas, was, a robber.