< Yohanna 18 >
1 Da ya gama addu’a, sai Yesu ya fita tare da almajiransa suka haye Kwarin Kidron. A wancan ƙetaren kuwa akwai lambun zaitun, da shi da almajiransa suka shiga ciki.
When Jesus had said these things, He went with His disciples across the Kidron ravine, where there was a garden, into which He and His disciples entered.
2 To, Yahuda, wanda ya bashe shi, ya san wurin, domin Yesu ya sha zuwa wurin da almajiransa.
Now Judas, who was betraying Him, also knew the place, because Jesus had often met there with His disciples.
3 Saboda haka Yahuda ya zo cikin lambun, yana jagoranta ƙungiyar sojoji da waɗansu ma’aikata daga wurin manyan firistoci da Farisiyawa. Suna riƙe da toci, fitilu da kuma makamai.
Then Judas, leading a detachment of soldiers and officers from the chief priests and Pharisees, came there with lanterns, torches, and weapons.
4 Yesu kuwa, sane da duk abin da zai same shi, ya fito ya tambaye, su ya ce, “Wa kuke nema?”
Therefore Jesus, knowing everything that would happen to Him, went forward and asked them, “Who are you looking for?”
5 Suka amsa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce, “Ni ne shi.” (Yahuda kuwa wanda ya bashe shi yana nan tsaye tare da su.)
They answered, “Jesus of Nazareth.” Jesus told them, “I AM.” Judas, who betrayed Him, also stood with them.
6 Da Yesu ya ce, “Ni ne shi,” sai suka ja da baya suka fāɗi a ƙasa.
Now when He told them, “I AM,” they drew back and fell to the ground.
7 Sai ya sāke tambayar su ya ce, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
Then He asked them again, “Who are you looking for?” They said, “Jesus of Nazareth.”
8 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku ni ne shi. In kuma ni ne kuke nema, to, sai ku bar waɗannan su tafi.”
Jesus answered, “I told you that I AM. So, if you are looking for me, let these go their way,”
9 Wannan ya faru ne don a cika kalmomin da ya yi cewa, “Ban yar da ko ɗaya daga cikin waɗanda ka ba ni ba.”
that the saying might be fulfilled which He spoke, “I have lost none of those who You gave me.”
10 Sai Siman Bitrus, wanda yake da takobi, ya zāre, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama (Sunan bawan kuwa Malkus ne.)
Then Simon Peter, having a sword, drew it and struck the high priest’s servant, and cut off his right ear. The servant’s name was Malchus.
11 Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
So Jesus told Peter, “Put your sword into its sheath! Shouldn’t I drink the cup that my Father has given me?”
12 Sai ƙungiyar soja tare da shugaban sojanta da kuma ma’aikatan Yahudawa suka kama Yesu. Suka daure shi
Then the detachment of soldiers and their commander and the officers of the Jews arrested Jesus and tied Him up.
13 sa’an nan suka kawo shi da farko wurin Annas, wanda yake surukin Kayifas, babban firist a shekaran nan.
They led Him away to Annas first, because he was the father-in-law of Caiaphas, who was high priest that year.
14 Kayifas ne wanda ya shawarci Yahudawa cewa zai fi kyau mutum ɗaya yă mutu saboda mutane.
It was Caiaphas who advised the Jews that it was expedient that one man should die for the people.
15 Siman Bitrus da kuma wani almajiri suna bin Yesu. Domin almajirin nan sananne ne ga babban firist, sai ya shiga tare da Yesu a filin gidan babban firist ɗin,
Simon Peter was following Jesus, and so was another disciple. Since the high priest knew that disciple, he entered with Jesus into the high priest’s court,
16 Bitrus kuwa ya dakata a waje a bakin ƙofa. Almajirin nan da yake sananne ga babban firist, ya dawo ya yi magana da yarinyar mai aiki a can, ya kuma shigo da Bitrus.
but Peter was standing just outside the door. So the other disciple, who the high priest knew, went out and spoke to the woman who guarded the door, and brought Peter in.
17 Yarinyar da take bakin ƙofar ta ce wa Bitrus, “Kai ba ɗaya ne daga cikin almajiran mutumin nan ba ne?” Bitrus ya amsa ya ce, “A’a, ba na ciki.”
Then the maidservant who kept the door asked Peter, “You aren’t one of this man’s disciples, too, are you?” He said, “I am not.”
18 To, ana sanyi, bayi da ma’aikatan suna tsattsaye kewaye da wutar da suka hura don su ji ɗumi. Bitrus ma yana tsaye tare da su, yana jin ɗumi.
Because it was cold, the servants and the officers were standing there warming themselves, having made a charcoal fire. Peter was also with them, standing and warming himself.
19 Ana cikin haka, sai babban firist ya tuhumi Yesu game da almajiransa da kuma koyarwarsa.
Then the high priest asked Jesus about His disciples and His doctrine.
20 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a fili. Na kuma sha yin koyarwa a majami’u ko kuma a haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban taɓa faɗin kome a ɓoye ba.
Jesus answered him, “I have spoken openly to the world. I always taught in synagogues, and in the temple, where all the Jews come together. I said nothing in secret.
21 Don me kake tuhumata? Ka tambayi waɗanda suka ji ni. Ba shakka, sun san abin da na faɗa.”
Why do you ask me? Ask those who have heard me to tell you what I told them. They certainly know what I said.”
22 Da Yesu ya faɗa haka, sai ɗaya daga cikin ma’aikatan da yake tsaye kusa ya mare shi a fuska ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?”
When He had said these things, one of the officers who stood by hit Jesus with the palm of his hand, saying, “Is that how you answer the high priest?”
23 Yesu ya amsa ya ce, “In na faɗi abin da ba daidai ba, ka nuna abin da ba daidai ba. Amma in gaskiya na faɗa, don me ka mare ni?”
Jesus answered him, “If I have spoken evil, testify about the evil, but if I have spoken honestly, why do you hit me?”
24 Sai Annas ya aika da shi, a daure, wurin Kayifas babban firist.
Then Annas sent Him, still bound, to Caiaphas, the high priest.
25 Da Siman Bitrus yana nan tsaye yana jin ɗumin wuta, sai aka tambaye shi, “Kai, kai ma ba ɗaya daga cikin almajiransa ba ne?” Sai ya yi mūsu, yana cewa, “Sam, ba na ciki.”
Now Simon Peter stood and warmed himself. Therefore they asked him, “You aren’t one of His disciples, too, are you?” He denied it, saying, “I am not!”
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist dangin wanda Bitrus ya sare wa kunne, ya tambaya shi ya ce, “Kana tsammani ban gan ka tare da shi a gonar zaitun ba?”
One of the servants of the high priest, a relative of the man whose ear Peter cut off, said, “Didn’t I see you in the garden with Him?”
27 Bitrus ya sāke yin mūsu, nan take kuwa zakara ya yi cara.
Peter then denied it again, and immediately a rooster crowed.
28 Sa’an nan Yahudawa suka fitar da Yesu daga wurin Kayifas zuwa fadar gwamnar Roma. A yanzu dai, safiya ta yi, don gudu kada su ƙazantar da kansu Yahudawa ba su shiga cikin fadar ba; sun so su iya ci Bikin Ƙetarewa.
Then they led Jesus from Caiaphas to the Praetorium. It was early morning. They themselves didn’t go into the Praetorium, so that they wouldn’t be defiled, and so that they might eat the Passover supper.
29 Saboda haka Bilatus ya fito wajensu ya ce, “Wace ƙara kuke kawowa game da mutumin nan?”
So Pilate came out to them and asked, “What charges do you bring against this man?”
30 Suka amsa suka ce, “Da a ce shi ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bashe shi gare ka ba.”
They answered, “If this man wasn’t a criminal, we wouldn’t have handed him over to you.”
31 Bilatus ya ce, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga dokarku.” Sai Yahudawa suka ƙi suka ce, “Ba mu da ikon yanke wa wani hukuncin kisa.”
Then Pilate told them, “You take Him and judge Him according to your Law.” Therefore the Jews said to him, “It’s illegal for us to put anyone to death.”
32 Wannan kuwa ya faru ne don a cika kalmomin da Yesu ya yi da suka nuna irin mutuwar da zai yi.
This happened so that the words would be fulfilled which Jesus had spoken indicating the kind of death he was going to die.
33 Sai Bilatus ya koma cikin fada, ya kira Yesu ya tambaye shi, “Shin, kai ne sarkin Yahudawa?”
Then Pilate went back into the Praetorium, summoned Jesus, and asked Him, “Are You the King of the Jews?”
34 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Wannan ra’ayin kanka ne, ko waɗansu ne suka yi maka magana game da ni?”
Jesus answered, “Are you speaking for yourself about this, or did others tell you this about me?”
35 Bilatus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne? Ai, mutanenka ne da kuma manyan firistoci suka bashe ka gare ni. Me ka yi?”
Pilate answered, “I’m not a Jew, am I? Your own nation and the chief priests have delivered You to me. What have You done?”
36 Yesu ya ce, “Mulkina ba na duniyan nan ba ne. Da na duniyan nan ne da bayina sun yi yaƙi su hana Yahudawa kama ni. Amma fa mulkina daga wani waje ne.”
Jesus answered, “My kingdom doesn’t belong to this world. If my kingdom did belong to this world, then my servants would be fighting to keep me from being delivered up to the Jews; but as it is, my kingdom isn’t from here.”
37 Sai Bilatus ya ce, “To, wato, kai sarki ne!” Yesu ya amsa ya ce, “Haka yake, ni sarki ne yadda ka faɗa. Tabbatacce, saboda wannan dalili ne aka haife ni, kuma don wannan ne na zo duniya, domin in shaidi gaskiya. Duk wanda yake gefen gaskiya yakan saurare ni.”
Pilate therefore asked Him, “So You are a king?” Jesus answered, “You are right in saying that I am a king. For this I have been born, and for this I have come into the world, to testify about the truth. Everyone who belongs to the truth listens to my voice.”
38 Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Mece ce gaskiya?” Da ya faɗi haka, sai ya sāke fitowa wurin Yahudawa ya ce, “Ni fa ban sami wani abin zargi game da shi ba.
“What is truth?” Pilate asked. After asking this, he went out again to the Jews and said, “I find no basis for a charge against Him,
39 Amma fa kuna da wata al’ada in lokacin Bikin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku da ɗan kurkuku ɗaya. To, kuna so in sakar muku ‘sarkin Yahudawa’?”
but you have a custom that I should release someone to you at the Passover. Therefore you decide: do you want me to release the King of the Jews to you?”
40 Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “Kai, ba shi ba! A ba mu Barabbas!” To, Barabbas ɗin nan yana da hannu dumu-dumu a wani tawaye.
Then they all shouted back, saying, “Not this man, but Barabbas!” Now Barabbas was a robber.