< Yohanna 18 >
1 Da ya gama addu’a, sai Yesu ya fita tare da almajiransa suka haye Kwarin Kidron. A wancan ƙetaren kuwa akwai lambun zaitun, da shi da almajiransa suka shiga ciki.
To když pověděl Ježíš, vyšel s učedlníky svými přes potok Cedron, kdež byla zahrada; do kteréžto všel on i učedlníci jeho.
2 To, Yahuda, wanda ya bashe shi, ya san wurin, domin Yesu ya sha zuwa wurin da almajiransa.
Věděl pak i Jidáš, zrádce jeho, to místo; nebo často chodíval tam Ježíš s učedlníky svými.
3 Saboda haka Yahuda ya zo cikin lambun, yana jagoranta ƙungiyar sojoji da waɗansu ma’aikata daga wurin manyan firistoci da Farisiyawa. Suna riƙe da toci, fitilu da kuma makamai.
Protož Jidáš pojav s sebou zástup, a od předních kněží a farizeů služebníky, přišel tam s lucernami a s pochodněmi a s zbrojí.
4 Yesu kuwa, sane da duk abin da zai same shi, ya fito ya tambaye, su ya ce, “Wa kuke nema?”
Ježíš pak věda všecko, což přijíti mělo na něj, vyšed proti nim, řekl jim: Koho hledáte?
5 Suka amsa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce, “Ni ne shi.” (Yahuda kuwa wanda ya bashe shi yana nan tsaye tare da su.)
Odpověděli jemu: Ježíše Nazaretského. Řekl jim Ježíš: Jáť jsem. Stál pak s nimi i Jidáš, zrádce jeho.
6 Da Yesu ya ce, “Ni ne shi,” sai suka ja da baya suka fāɗi a ƙasa.
A jakž řekl jim: Já jsem, postoupili nazpět, a padli na zem.
7 Sai ya sāke tambayar su ya ce, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
I otázal se jich opět: Koho hledáte? A oni řekli: Ježíše Nazaretského.
8 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku ni ne shi. In kuma ni ne kuke nema, to, sai ku bar waɗannan su tafi.”
Odpověděl Ježíš: Pověděl jsem vám, že já jsem. Poněvadž tedy mne hledáte, nechtež těchto, ať odejdou.
9 Wannan ya faru ne don a cika kalmomin da ya yi cewa, “Ban yar da ko ɗaya daga cikin waɗanda ka ba ni ba.”
Aby se naplnila řeč, kterouž byl pověděl: Že které jsi mi dal, neztratil jsem z nich žádného.
10 Sai Siman Bitrus, wanda yake da takobi, ya zāre, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama (Sunan bawan kuwa Malkus ne.)
Tedy Šimon Petr, maje meč, vytrhl jej a udeřil služebníka nejvyššího kněze a uťal mu ucho jeho pravé. A bylo jméno služebníka toho Malchus.
11 Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
I řekl Ježíš Petrovi: Schovej meč svůj do pošvy. Což nemám píti kalicha, kterýž mi dal Otec?
12 Sai ƙungiyar soja tare da shugaban sojanta da kuma ma’aikatan Yahudawa suka kama Yesu. Suka daure shi
Tedy zástup a hejtman a služebníci Židovští jali Ježíše, a svázali jej.
13 sa’an nan suka kawo shi da farko wurin Annas, wanda yake surukin Kayifas, babban firist a shekaran nan.
A vedli ho k Annášovi nejprve; nebo byl test Kaifášův, kterýž byl nejvyšším knězem toho léta.
14 Kayifas ne wanda ya shawarci Yahudawa cewa zai fi kyau mutum ɗaya yă mutu saboda mutane.
Kaifáš pak byl ten, kterýž byl radu dal Židům, že by užitečné bylo, aby člověk jeden umřel za lid.
15 Siman Bitrus da kuma wani almajiri suna bin Yesu. Domin almajirin nan sananne ne ga babban firist, sai ya shiga tare da Yesu a filin gidan babban firist ɗin,
Šel pak za Ježíšem Šimon Petr a jiný učedlník. A ten učedlník byl znám nejvyššímu knězi, i všel s Ježíšem do síně nejvyššího kněze.
16 Bitrus kuwa ya dakata a waje a bakin ƙofa. Almajirin nan da yake sananne ga babban firist, ya dawo ya yi magana da yarinyar mai aiki a can, ya kuma shigo da Bitrus.
Ale Petr stál u dveří vně. I vyšel ten druhý učedlník, kterýž byl znám nejvyššímu knězi, a promluvil s vrátnou, i uvedl tam Petra.
17 Yarinyar da take bakin ƙofar ta ce wa Bitrus, “Kai ba ɗaya ne daga cikin almajiran mutumin nan ba ne?” Bitrus ya amsa ya ce, “A’a, ba na ciki.”
Tedy řekla Petrovi děvečka vrátná: Nejsi-liž i ty z učedlníků člověka toho? Řekl on: Nejsem.
18 To, ana sanyi, bayi da ma’aikatan suna tsattsaye kewaye da wutar da suka hura don su ji ɗumi. Bitrus ma yana tsaye tare da su, yana jin ɗumi.
Stáli pak tu služebníci a pacholci, kteříž oheň udělali, nebo zima bylo, i zhřívali se. A byl s nimi také i Petr, stoje tu a zhřívaje se.
19 Ana cikin haka, sai babban firist ya tuhumi Yesu game da almajiransa da kuma koyarwarsa.
Tedy nejvyšší kněz tázal se Ježíše o učedlnících jeho a o učení jeho.
20 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a fili. Na kuma sha yin koyarwa a majami’u ko kuma a haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban taɓa faɗin kome a ɓoye ba.
Odpověděl jemu Ježíš: Já zjevně mluvil jsem světu, já vždycky učíval jsem v škole a v chrámě, kdežto se odevšad Židé scházejí, a tajně jsem nic nemluvil,
21 Don me kake tuhumata? Ka tambayi waɗanda suka ji ni. Ba shakka, sun san abin da na faɗa.”
Co se mne ptáš? Ptej se těch, kteříž mne slýchali, co jsem jim mluvil. Aj, tiť vědí, co jsem já mluvil.
22 Da Yesu ya faɗa haka, sai ɗaya daga cikin ma’aikatan da yake tsaye kusa ya mare shi a fuska ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?”
A když on to pověděl, jeden z služebníků, stoje tu, dal poliček Ježíšovi, řka: Tak-liž odpovídáš nejvyššímu knězi?
23 Yesu ya amsa ya ce, “In na faɗi abin da ba daidai ba, ka nuna abin da ba daidai ba. Amma in gaskiya na faɗa, don me ka mare ni?”
Odpověděl mu Ježíš: Mluvil-li jsem zle, svědectví vydej o zlém; pakli dobře, proč mne tepeš?
24 Sai Annas ya aika da shi, a daure, wurin Kayifas babban firist.
I poslal jej Annáš svázaného k Kaifášovi nejvyššímu knězi.
25 Da Siman Bitrus yana nan tsaye yana jin ɗumin wuta, sai aka tambaye shi, “Kai, kai ma ba ɗaya daga cikin almajiransa ba ne?” Sai ya yi mūsu, yana cewa, “Sam, ba na ciki.”
Stál pak Šimon Petr, a zhříval se. Tedy řekli jemu: Nejsi-liž i ty z učedlníků jeho? Zapřel on a řekl: Nejsem.
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist dangin wanda Bitrus ya sare wa kunne, ya tambaya shi ya ce, “Kana tsammani ban gan ka tare da shi a gonar zaitun ba?”
Dí jemu jeden z služebníků nejvyššího kněze, příbuzný toho, kterémuž Petr uťal ucho: Zdaž jsem já tebe neviděl s ním v zahradě?
27 Bitrus ya sāke yin mūsu, nan take kuwa zakara ya yi cara.
Tedy Petr opět zapřel. A hned kohout zazpíval.
28 Sa’an nan Yahudawa suka fitar da Yesu daga wurin Kayifas zuwa fadar gwamnar Roma. A yanzu dai, safiya ta yi, don gudu kada su ƙazantar da kansu Yahudawa ba su shiga cikin fadar ba; sun so su iya ci Bikin Ƙetarewa.
I vedli Ježíše od Kaifáše do radného domu, a bylo ráno. Oni pak nevešli do radného domu, aby se neposkvrnili, ale aby jedli beránka.
29 Saboda haka Bilatus ya fito wajensu ya ce, “Wace ƙara kuke kawowa game da mutumin nan?”
Tedy vyšel k nim Pilát ven a řekl: Jakou žalobu vedete proti člověku tomuto?
30 Suka amsa suka ce, “Da a ce shi ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bashe shi gare ka ba.”
Odpověděli a řekli jemu: Byť tento nebyl zločinec, nedali bychom ho tobě.
31 Bilatus ya ce, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga dokarku.” Sai Yahudawa suka ƙi suka ce, “Ba mu da ikon yanke wa wani hukuncin kisa.”
I řekl jim Pilát: Vezměte vy jej, a podle Zákona vašeho suďte ho. I řekli mu Židé: Námť nesluší zabíti žádného.
32 Wannan kuwa ya faru ne don a cika kalmomin da Yesu ya yi da suka nuna irin mutuwar da zai yi.
Aby se řeč Ježíšova naplnila, kterouž řekl, znamenaje, kterou by smrtí měl umříti.
33 Sai Bilatus ya koma cikin fada, ya kira Yesu ya tambaye shi, “Shin, kai ne sarkin Yahudawa?”
Tedy Pilát všel opět do radného domu, i povolal Ježíše a řekl jemu: Ty-li jsi Král Židovský?
34 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Wannan ra’ayin kanka ne, ko waɗansu ne suka yi maka magana game da ni?”
Odpověděl Ježíš: Sám-li od sebe to pravíš, čili jiní tobě pověděli o mně?
35 Bilatus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne? Ai, mutanenka ne da kuma manyan firistoci suka bashe ka gare ni. Me ka yi?”
Odpověděl Pilát: Zdaliž jsem já Žid? Národ tvůj a přední kněží dali mi tebe. Co jsi učinil?
36 Yesu ya ce, “Mulkina ba na duniyan nan ba ne. Da na duniyan nan ne da bayina sun yi yaƙi su hana Yahudawa kama ni. Amma fa mulkina daga wani waje ne.”
Odpověděl Ježíš: Království mé není z tohoto světa. Byť z tohoto světa bylo království mé, služebníci moji bránili by mne, abych nebyl vydán Židům. Ale nyní mé království není odsud.
37 Sai Bilatus ya ce, “To, wato, kai sarki ne!” Yesu ya amsa ya ce, “Haka yake, ni sarki ne yadda ka faɗa. Tabbatacce, saboda wannan dalili ne aka haife ni, kuma don wannan ne na zo duniya, domin in shaidi gaskiya. Duk wanda yake gefen gaskiya yakan saurare ni.”
I řekl jemu Pilát: Tedy král jsi ty? Dí Ježíš: Ty pravíš, že já král jsem. Jáť jsem se k tomu narodil, a proto jsem na svět přišel, abych svědectví vydal pravdě. Každý, kdož jest z pravdy, slyší hlas můj.
38 Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Mece ce gaskiya?” Da ya faɗi haka, sai ya sāke fitowa wurin Yahudawa ya ce, “Ni fa ban sami wani abin zargi game da shi ba.
Dí jemu Pilát: Co jest pravda? A když to řekl, opět vyšel k Židům, a dí jim: Já na něm žádné viny nenalézám.
39 Amma fa kuna da wata al’ada in lokacin Bikin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku da ɗan kurkuku ɗaya. To, kuna so in sakar muku ‘sarkin Yahudawa’?”
Ale jest obyčej váš, abych vám propustil jednoho vězně na velikunoc. Chcete-liž tedy, ať vám propustím Krále Židovského?
40 Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “Kai, ba shi ba! A ba mu Barabbas!” To, Barabbas ɗin nan yana da hannu dumu-dumu a wani tawaye.
I zkřikli opět všickni, řkouce: Ne toho, ale Barabbáše. Byl pak Barabbáš lotr.