< Yohanna 17 >
1 Bayan da Yesu ya faɗi wannan, sai ya dubi sama ya yi addu’a ya ce, “Uba, lokaci ya yi. Ka ɗaukaka Ɗanka, don Ɗanka yă ɗaukaka ka.
Jesus said these things; then, lifting his eyes to heaven, he said, Father, the time has now come; give glory to your Son, so that the Son may give glory to you:
2 Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. (aiōnios )
Even as you gave him authority over all flesh, to give eternal life to all those whom you have given to him. (aiōnios )
3 Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. (aiōnios )
And this is eternal life: to have knowledge of you, the only true God, and of him whom you have sent, even Jesus Christ. (aiōnios )
4 Na ɗaukaka ka a duniya ta wurin gama aikin da ka ba ni.
I have given you glory on the earth, having done all the work which you gave me to do.
5 Yanzu ya Uba, ka ɗaukaka ni a gabanka da ɗaukakar da dā nake da ita tun kafin a kafa duniya.
And now, Father, let me have glory with you, even that glory which I had with you before the world was.
6 “Na bayyana ka ga waɗanda ka ba ni a duniya. Su naka ne; kai ka ba ni su sun kuma yi biyayya da maganarka.
I have given knowledge of your name to the men whom you gave me out of the world: yours they were, and you gave them to me, and they have kept your words.
7 Yanzu sun san cewa duk abin da ka ba ni daga gare ka ya fito.
Now it is clear to them that whatever you have given to me comes from you:
8 Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni.
Because I have given them the words which you gave to me; and they have taken them to heart, and have certain knowledge that I came from you, and they have faith that you sent me.
9 Ina addu’a dominsu. Ba domin duniya nake addu’a ba, amma domin waɗanda ka ba ni, gama su naka ne.
My prayer is for them: my prayer is not for the world, but for those whom you have given to me, because they are yours
10 Duk abin da nake da shi naka ne, kuma duk abin da kake da shi nawa ne. Na kuwa sami ɗaukaka ta wurinsu.
(All mine are yours, and yours are mine) and I have glory in them.
11 Ba sauran zamana a duniya, amma waɗannan a duniya suke, ni kuwa ina zuwa wurinka. Ya Uba Mai Tsarki, ka kiyaye su ta wurin ikon sunanka, sunan da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
And now I will be no longer in the world, but they are in the world and I come to you. Holy Father, keep them in your name which you have given to me, so that they may be one even as we are one.
12 Yayinda nake tare da su, na kāre su na kuma kiyaye su ta wurin sunan nan da ka ba ni. Ba ko ɗayan da ya ɓace, sai dai wannan da aka ƙaddara zuwa ga hallaka don Nassi yă cika.
While I was with them I kept them safe in your name which you have given to me: I took care of them and not one of them has come to destruction, but only the son of destruction, so that the Writings might come true.
13 “Yanzu ina zuwa wurinka, sai dai na faɗi waɗannan abubuwa ne tun ina a duniya domin farin ciki yă zama cikakke a cikinsu.
And now I come to you; and these things I say in the world so that they may have my joy complete in them.
14 Na gaya musu maganarka duniya kuwa ta ƙi su, don su ba na duniya ba ne yadda ni ma ba na duniya ba ne.
I have given your word to them; and they are hated by the world, because they are not of the world, even as I am not of the world.
15 Ba addu’ata ba ce ka ɗauke su daga duniya ba, sai dai ka kāre su daga mugun nan.
My prayer is not that you will take them out of the world, but that you will keep them from the Evil One.
16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne.
They are not of the world any more than I am of the world.
17 Ka tsarkake su ta wurin gaskiya; maganarka ce gaskiya.
Make them holy by the true word: your word is the true word.
18 Kamar yadda ka aiko ni cikin duniya, haka ni ma na aike su cikin duniya.
Even as you have sent me into the world, so I have sent them into the world.
19 Saboda su ne na tsarkake kaina, domin su ma a tsarkake su da gaske.
And for them I make myself holy, so that they may be made truly holy.
20 “Addu’ata ba saboda masu bina kaɗai ba ne. Ina addu’a kuma saboda waɗanda za su gaskata da ni ta wurin maganarsu.
My prayer is not for them only, but for all who will have faith in me through their word;
21 Ina so dukansu su zama ɗaya, ya Uba, kamar yadda kake a cikina, ni kuwa a cikinka. Haka su ma bari su zauna cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa kai ka aiko ni.
May they all be one! Even as you, Father, are in me and I am in you, so let them be in us, so that all men may come to have faith that you sent me.
22 Na ba su ɗaukakar da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
And the glory which you have given to me I have given to them, so that they may be one even as we are one;
23 Ni a cikinsu kai kuma a cikina. Bari su kasance da cikakken haɗinkai, domin duniya ta san cewa kai ka aiko ni. Ka kuwa ƙaunace su yadda ka ƙaunace ni.
I in them, and you in me, so that they may be made completely one, and so that it may become clear to all men that you have sent me and that they are loved by you as I am loved by you.
24 “Uba, ina so waɗanda ka ba ni su kasance tare da ni a inda nake, su kuma ga ɗaukakata, ɗaukakar da ka ba ni domin kana ƙaunata kafin halittar duniya.
Father, it is my desire that these whom you have given to me may be by my side where I am, so that they may see my glory which you have given to me, because you had love for me before the world came into being.
25 “Ya Uba Mai Adalci, ko da yake duniya ba tă san ka ba, ni na san ka, sun kuma san kai ka aiko ni.
Father of righteousness, I have knowledge of you, though the world has not; and to these it is clear that you sent me;
26 Na bayyana ka a gare su, zan kuma ci gaba da bayyana ka domin ƙaunar da ka yi mini ta kasance a cikinsu ni ma in kasance a cikinsu.”
And I have given to them knowledge of your name, and will give it, so that the love which you have for me may be in them and I in them.