< Yohanna 17 >
1 Bayan da Yesu ya faɗi wannan, sai ya dubi sama ya yi addu’a ya ce, “Uba, lokaci ya yi. Ka ɗaukaka Ɗanka, don Ɗanka yă ɗaukaka ka.
To pověděv Ježíš, i pozdvihl oči svých k nebi a řekl: Otče, přišlať hodina, oslaviž Syna svého, aby i Syn tvůj oslavil tebe;
2 Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. (aiōnios )
Jakož jsi dal jemu moc nad každým člověkem, aby těm všechněm, kteréž jsi dal jemu, život věčný dal. (aiōnios )
3 Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. (aiōnios )
Totoť jest pak věčný život, aby poznali tebe samého pravého Boha, a kteréhož jsi poslal, Ježíše Krista. (aiōnios )
4 Na ɗaukaka ka a duniya ta wurin gama aikin da ka ba ni.
Jáť jsem oslavil tebe na zemi; dílo jsem vykonal, kteréž jsi mi dal, abych činil.
5 Yanzu ya Uba, ka ɗaukaka ni a gabanka da ɗaukakar da dā nake da ita tun kafin a kafa duniya.
A nyní oslaviž ty mne, Otče, u sebe samého touž slavou, kterouž jsem měl u tebe, prvé nežli svět byl.
6 “Na bayyana ka ga waɗanda ka ba ni a duniya. Su naka ne; kai ka ba ni su sun kuma yi biyayya da maganarka.
Oznámil jsem jméno tvé lidem, kteréž jsi mi dal z světa. Tvojiť byli, a mně jsi je dal, a řeč tvou zachovali.
7 Yanzu sun san cewa duk abin da ka ba ni daga gare ka ya fito.
A nyní poznali, že všecky věci, kteréž jsi mi dal, od tebe jsou.
8 Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni.
Nebo slova, kteráž jsi mi dal, dal jsem jim; a oni přijali, a poznali právě, že jsem od tebe vyšel, a uvěřili, že jsi ty mne poslal.
9 Ina addu’a dominsu. Ba domin duniya nake addu’a ba, amma domin waɗanda ka ba ni, gama su naka ne.
Já za ně prosím, ne za svět prosím, ale za ty, kteréž jsi mi dal, nebo tvoji jsou.
10 Duk abin da nake da shi naka ne, kuma duk abin da kake da shi nawa ne. Na kuwa sami ɗaukaka ta wurinsu.
A všecky věci mé tvé jsou, a tvé mé jsou, a oslaven jsem v nich.
11 Ba sauran zamana a duniya, amma waɗannan a duniya suke, ni kuwa ina zuwa wurinka. Ya Uba Mai Tsarki, ka kiyaye su ta wurin ikon sunanka, sunan da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
Již pak více nejsem na světě, ale oni jsou na světě, a já k tobě jdu. Otče svatý, ostříhejž jich ve jménu svém, kteréž jsi mi dal, aťby byli jedno jako my.
12 Yayinda nake tare da su, na kāre su na kuma kiyaye su ta wurin sunan nan da ka ba ni. Ba ko ɗayan da ya ɓace, sai dai wannan da aka ƙaddara zuwa ga hallaka don Nassi yă cika.
Dokudž jsem s nimi byl na světě, já jsem jich ostříhal ve jménu tvém. Kteréž jsi mi dal, zachoval jsem, a žádný z nich nezahynul, než syn zatracení, aby se písmo naplnilo.
13 “Yanzu ina zuwa wurinka, sai dai na faɗi waɗannan abubuwa ne tun ina a duniya domin farin ciki yă zama cikakke a cikinsu.
Ale nyní k tobě jdu, a toto mluvím na světě, aby měli radost mou plnou v sobě.
14 Na gaya musu maganarka duniya kuwa ta ƙi su, don su ba na duniya ba ne yadda ni ma ba na duniya ba ne.
Já jsem jim dal slovo tvé, a svět jich nenáviděl; nebo nejsou z světa, jako já nejsem z světa.
15 Ba addu’ata ba ce ka ɗauke su daga duniya ba, sai dai ka kāre su daga mugun nan.
Neprosímť, abys je vzal z světa, ale abys je zachoval od toho zlého.
16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne.
Z světať nejsou, jako i já nejsem z světa.
17 Ka tsarkake su ta wurin gaskiya; maganarka ce gaskiya.
Posvětiž jich v pravdě své, slovo tvé pravda jest.
18 Kamar yadda ka aiko ni cikin duniya, haka ni ma na aike su cikin duniya.
Jakož jsi mne poslal na svět, i já jsem je poslal na svět.
19 Saboda su ne na tsarkake kaina, domin su ma a tsarkake su da gaske.
A já posvěcuji sebe samého za ně, aby i oni posvěceni byli v pravdě.
20 “Addu’ata ba saboda masu bina kaɗai ba ne. Ina addu’a kuma saboda waɗanda za su gaskata da ni ta wurin maganarsu.
Ne za tytoť pak toliko prosím, ale i za ty, kteříž skrze slovo jejich mají uvěřiti ve mne,
21 Ina so dukansu su zama ɗaya, ya Uba, kamar yadda kake a cikina, ni kuwa a cikinka. Haka su ma bari su zauna cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa kai ka aiko ni.
Aby všickni jedno byli, jako ty, Otče, ve mně, a já v tobě, aby i oni v nás jedno byli, aby uvěřil svět, že jsi ty mne poslal.
22 Na ba su ɗaukakar da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
A já slávu, kterouž jsi mi dal, dal jsem jim, aby byli jedno, jako my jedno jsme.
23 Ni a cikinsu kai kuma a cikina. Bari su kasance da cikakken haɗinkai, domin duniya ta san cewa kai ka aiko ni. Ka kuwa ƙaunace su yadda ka ƙaunace ni.
Já v nich, a ty ve mně, aby dokonáni byli v jedno, a aby poznal svět, že jsi ty mne poslal, a že jsi je miloval, jakožs mne miloval.
24 “Uba, ina so waɗanda ka ba ni su kasance tare da ni a inda nake, su kuma ga ɗaukakata, ɗaukakar da ka ba ni domin kana ƙaunata kafin halittar duniya.
Otče, kteréž jsi mi dal, chciť, kdež jsem já, aby i oni byli se mnou, aby hleděli na slávu mou, kteroužs mi dal; nebo jsi mne miloval před ustanovením světa.
25 “Ya Uba Mai Adalci, ko da yake duniya ba tă san ka ba, ni na san ka, sun kuma san kai ka aiko ni.
Otče spravedlivý, tebeť svět nepoznal, ale já jsem tebe poznal, a i tito poznali, že jsi ty mne poslal.
26 Na bayyana ka a gare su, zan kuma ci gaba da bayyana ka domin ƙaunar da ka yi mini ta kasance a cikinsu ni ma in kasance a cikinsu.”
A známéť jsem jim učinil jméno tvé, a známo učiním, aby milování, kterýmž jsi mne miloval, bylo v nich, a i já v nich.