< Yohanna 16 >
1 “Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
To sem vam povedal, da se ne pohujšate.
2 Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
Izganjali vas bodo iz shajališč: prišel pa bo čas, da bo vsak, kdor vas bo moril, menil, da Bogu služi.
3 Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
In to vam bodo delali, ker niso poznali očeta ne mene.
4 Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
Ali to sem vam povedal, da se boste, kedar ta čas pride, spomenili tega, da sem vam jaz povedal; tega vam pa od začetka nisem povedal, ker sem z vami bil.
5 “Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
A sedaj grem k temu, kteri me je poslal, in nobeden od vas me ne vpraša: Kam greš?
6 Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
Temveč ker sem vam to povedal, napolnila vam je žalost srce.
7 Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
Ali jaz vam po pravici pravim: Bolje vam je, da jaz odidem. Kajti če ne odidem, ne bo prišel tolažnik k vam; če pa odidem, poslal vam ga bom.
8 Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
In kedar on pride, prepričal bo svet greha in pravice in sodbe.
9 a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
Greha namreč, ker ne verujejo v mé:
10 a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
Pravice pa, ker grem k očetu svojemu, in me ne boste več videli;
11 a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
A sodbe, ker je vojvoda tega sveta obsojen.
12 “Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
Še veliko vam imam povedati; pa sedaj ne morete nositi.
13 Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
Kedar pa on pride, Duh resnice, napotil vas bo na vsako resnico; ne bo namreč govoril od sebe, nego govoril bo, kar bo slišal, in oznanjeval vam bo prihodnje rečí.
14 Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
On bo mene oslavil, ker bo od mojega vzel in vam oznanil.
15 Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’”
Vse, kar ima oče, moje je; za to sem rekel, da bo od mojega vzel in vam oznanil
16 Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
Malo, in ne boste me videli; in zopet malo, in videli me boste; ker jaz grem k očetu.
17 A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
Tedaj rekó nekteri od učencev njegovih med seboj: Kaj je to, kar nam pravi: Malo, in ne boste me videli; in zopet malo, in videli me boste? in: Ker jaz grem k očetu?
18 Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”
In govorili so: Kaj je to, kar pravi: malo? Ne vémo, kaj pravi.
19 Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’?
Jezus pa spozná, da ga hočejo vprašati, in reče jim: Ali za to se pohujšujete med seboj, ker sem rekel: Malo, in ne boste me videli; in zopet malo, in videli me boste?
20 Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.
Resnično resnično vam pravim, da boste jokali vi in plakali, in svet se bo radoval; a vi boste žalostni: ali žalost vaša se bo premenila v radost.
21 Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya.
Žena, kedar rodí, ima žalost, ker je čas nje prišel; ali kedar porodí dete, ne spominja se več britkosti, od radosti, da se je rodil človek na svet.
22 Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku.
Tako tudi vas sedaj žalost objemlje; pa zopet vas bom videl, in srce vaše se bo radovalo, in radosti vaše vam ne bo nihče odvzel.
23 A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana.
In tisti dan me ne boste ničesar vpraševali. Resnično resnično vam pravim, da karkoli boste očeta v ime moje prosili, dal vam bo.
24 Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.
Doslej niste v ime moje ničesar prosili. Prosite, in prejeli boste, da bo radost vaša dopolnjena.
25 “Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana.
To sem vam povedal v prilikah; ali prišel bo čas, ko vam ne bom več govoril v prilikah, nego vam bom odkrito oznanjeval za očeta.
26 A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba.
Tisti dan boste v ime moje prosili; in ne pravim vam, da bom jaz prosil očeta za vas:
27 Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito.
Kajti oče vas sam ljubi, ker ste vi mene ljubili, in ste verovali, da sem jaz izšel od Boga.
28 Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”
Izšel sem od očeta, in prišel sem na svet; in zopet zapuščam svet, in grem k očetu.
29 Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba.
Rekó mu učenci njegovi; Glej, sedaj razločno govoriš, in prilike nobene ne praviš.
30 Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”
Sedaj vémo, da vse véš, in ti ni treba, da bi te kdo vpraševal. Po tem ti verujemo, da si od Boga izšel.
31 Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata!
Odgovorí jim Jezus: Ali sedaj verujete?
32 Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.
Glej, prišel bo čas, in sedaj je prišel, da se boste razkropili vsak na svojo stran in mene boste samega pustili; pa nisem sam, ker je oče z menoj.
33 “Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”
To sem vam povedal, da boste mir imeli v meni. Na svetu boste britkost imeli; ali ne bojte se, jaz sem svet premagal.