< Yohanna 16 >
1 “Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
'These things I have spoken to you, that ye may not be stumbled,
2 Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
out of the synagogues they will put you; but an hour doth come, that every one who hath killed you, may think to offer service unto God;
3 Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
and these things they will do to you, because they did not know the Father, nor me.
4 Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
'But these things I have spoken to you, that when the hour may come, ye may remember them, that I said [them] to you, and these things to you from the beginning I did not say, because I was with you;
5 “Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
and now I go away to Him who sent me, and none of you doth ask me, Whither dost thou go?
6 Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
but because these things I have said to you, the sorrow hath filled your heart.
7 Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
'But I tell you the truth; it is better for you that I go away, for if I may not go away, the Comforter will not come unto you, and if I go on, I will send Him unto you;
8 Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
and having come, He will convict the world concerning sin, and concerning righteousness, and concerning judgment;
9 a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
concerning sin indeed, because they do not believe in me;
10 a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
and concerning righteousness, because unto my Father I go away, and no more do ye behold me;
11 a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
and concerning judgment, because the ruler of this world hath been judged.
12 “Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
'I have yet many things to say to you, but ye are not able to bear [them] now;
13 Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
and when He may come — the Spirit of truth — He will guide you to all the truth, for He will not speak from Himself, but as many things as He will hear He will speak, and the coming things He will tell you;
14 Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
He will glorify me, because of mine He will take, and will tell to you.
15 Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’”
'All things, as many as the Father hath, are mine; because of this I said, That of mine He will take, and will tell to you;
16 Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
a little while, and ye do not behold me, and again a little while, and ye shall see me, because I go away unto the Father.'
17 A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
Therefore said [some] of his disciples one to another, 'What is this that he saith to us, A little while, and ye do not behold me, and again a little while, and ye shall see me, and, Because I go away unto the Father?'
18 Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”
they said then, 'What is this he saith — the little while? we have not known what he saith.'
19 Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’?
Jesus, therefore, knew that they were wishing to ask him, and he said to them, 'Concerning this do ye seek one with another, because I said, A little while, and you do not behold me, and again a little while, and ye shall see me?
20 Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.
verily, verily, I say to you, that ye shall weep and lament, and the world will rejoice; and ye shall be sorrowful, but your sorrow joy will become.
21 Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya.
'The woman, when she may bear, hath sorrow, because her hour did come, and when she may bear the child, no more doth she remember the anguish, because of the joy that a man was born to the world.
22 Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku.
'And ye, therefore, now, indeed, have sorrow; and again I will see you, and your heart shall rejoice, and your joy no one doth take from you,
23 A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana.
and in that day ye will question me nothing; verily, verily, I say to you, as many things as ye may ask of the Father in my name, He will give you;
24 Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.
till now ye did ask nothing in my name; ask, and ye shall receive, that your joy may be full.
25 “Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana.
'These things in similitudes I have spoken to you, but there cometh an hour when no more in similitudes will I speak to you, but freely of the Father, will tell you.
26 A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba.
'In that day, in my name ye will make request, and I do not say to you that I will ask the Father for you,
27 Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito.
for the Father himself doth love you, because me ye have loved, and ye have believed that I from God came forth;
28 Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”
I came forth from the Father, and have come to the world; again I leave the world, and go on unto the Father.'
29 Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba.
His disciples say to him, 'Lo, now freely thou dost speak, and no similitude speakest thou;
30 Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”
now we have known that thou hast known all things, and hast no need that any one do question thee; in this we believe that from God thou didst come forth.'
31 Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata!
Jesus answered them, 'Now do ye believe? lo, there doth come an hour,
32 Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.
and now it hath come, that ye may be scattered, each to his own things, and me ye may leave alone, and I am not alone, because the Father is with me;
33 “Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”
these things I have spoken to you, that in me ye may have peace, in the world ye shall have tribulation, but take courage — I have overcome the world.'