< Yohanna 16 >

1 “Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
"These things I have spoken to you in order to clear stumbling-blocks out of your path.
2 Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
You will be excluded from the synagogues; nay more, the time is coming when any one who has murdered one of you will suppose he is offering service to God.
3 Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
And they will do these things because they have failed to recognize the Father and to discover who I am.
4 Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
But I have spoken these things to you in order that when the time for their accomplishment comes you may remember them, and may recollect that I told you. I did not, however, tell you all this at first, because I was still with you.
5 “Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
But now I an returning to Him who sent me; and not one of you asks me where I am going.
6 Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
But grief has filled your hearts because I have said all this to you.
7 Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
"Yet it is the truth that I am telling you--it is to your advantage that I go away. For unless I go away, the Advocate will not come to you; but if I go, I will send Him to you.
8 Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
And He, when He comes, will convict the world in respect of sin, of righteousness, and of judgement; --
9 a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
of sin, because they do not believe in me;
10 a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
of righteousness, because I am going to the Father, and you will no longer see me;
11 a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
of judgement, because the Prince of this world is under sentence.
12 “Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
"I have much more to say to you, but you are unable at present to bear the burden of it.
13 Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
But when He has come--the Spirit of Truth--He will guide you into all the truth. For He will not speak as Himself originating what He says, but all that He hears He will speak, and He will make known the future to you.
14 Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
He will glorify me, because He will take of what is mine and will make it known to you.
15 Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’”
Everything that the Father has is mine; that is why I said that the Spirit of Truth takes of what is mine and will make it known to you.
16 Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
"A little while and you see me no more, and again a little while and you shall see me."
17 A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
Some of His disciples therefore said to one another, "What does this mean which He is telling us, 'A little while and you do not see me, and again a little while and you shall see me,' and 'Because I am going to the Father'?"
18 Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”
So they asked one another repeatedly, "What can that 'little while' mean which He speaks of? We do not understand His words."
19 Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’?
Jesus perceived that they wanted to ask Him, and He said, "Is this what you are questioning one another about--my saying, 'A little while and you do not see me, and again a little while and you shall see me'?
20 Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.
In most solemn truth I tell you that you will weep aloud and lament, but the world will be glad. You will mourn, but your grief will be turned into gladness.
21 Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya.
A woman, when she is in labour, has sorrow, because her time has come. But when she has given birth to the babe, she no longer remembers the pain, because of her joy at a child being born into the world.
22 Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku.
So you also now have sorrow; but I shall see you again, and your hearts will be glad, and your gladness no one will take away from you.
23 A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana.
You will put no questions to me then. "In most solemn truth I tell you that whatever you ask the Father for in my name He will give you.
24 Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.
As yet you have not asked for anything in my name: ask, and you shall receive, that your hearts may be filled with gladness.
25 “Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana.
"All this I have spoken to you in veiled language. The time is coming when I shall no longer speak to you in veiled language, but will tell you about the Father in plain words.
26 A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba.
At that time you will make your requests in my name; and I do not promise to ask the Father on your behalf,
27 Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito.
for the Father Himself holds you dear, because you have held me dear and have believed that I came from the Father's presence.
28 Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”
I came from the Father and have come into the world. Again I am leaving the world and am going to the Father."
29 Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba.
"Ah, now you are using plain language," said His disciples, "and are uttering no figure of speech!
30 Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”
Now we know that you have all knowledge, and do not need to be pressed with questions. Through this we believe that you came from God."
31 Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata!
"Do you at last believe?" replied Jesus.
32 Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.
"Remember that the time is coming, nay, has already come, for you all to be dispersed each to his own home and to leave me alone. And yet I am not alone, for the Father is with me.
33 “Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”
"I have spoken all this to you in order that in me you may have peace. In the world you have affliction. But keep up your courage: I have won the victory over the world."

< Yohanna 16 >