< Yohanna 15 >

1 “Ni ne kuringar inabi na gaskiya, Ubana kuwa shi ne manomin.
"Ich bin der wahre Weinstock; mein Vater ist der Weingärtner.
2 Yakan sare kowane reshe a cikina da ba ya’ya’ya, amma yakan ƙundume kowane reshe da yake ba da’ya’ya, domin yă ƙara ba da’ya’ya.
Er schneidet jeden Rebzweig an mir ab, der keine Frucht bringt; jeden aber, der Frucht trägt, reinigt er, damit er noch mehr Frucht trage.
3 Kun riga kun zama masu tsabta saboda maganar da na yi muku.
Ihr seid schon rein des Wortes wegen, das ich zu euch gesprochen habe.
4 Ku kasance a cikina, ni kuma zan kasance a cikinku. Babu reshen da zai iya yin’ya’ya da kansa, dole yă kasance a jikin kuringar inabin. Haka ku ma, ba za ku iya ba da’ya’ya ba sai kun kasance a cikina.
Bleibt in mir, dann bleibe ich in euch. Wie der Rebzweig aus sich selbst keine Frucht bringen kann, wenn er nicht am Weinstock bleibt, also auch ihr nicht, wenn ihr nicht in mir bleibt.
5 “Ni ne kuringar inabin; ku ne kuma rassan. In mutum ya kasance a cikina ni kuma a cikinsa, zai ba da’ya’ya da yawa; in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
Ich bin der Weinstock; ihr seid die Rebzweige. Wer in mir bleibt, und der, in dem ich bleibe, bringt viel Frucht; getrennt von mir, könnt ihr nichts tun.
6 Duk wanda bai kasance a cikina ba, yana kamar reshen da aka jefar yă bushe; irin waɗannan rassan ne akan tattara, a jefa cikin wuta a ƙone.
Wer nicht in mir bleibt, wird wie ein Rebzweig weggeworfen und verdorrt; man sucht sie dann zusammen, wirft sie ins Feuer und verbrennt sie.
7 In kun kasance a cikina kalmomina kuma suka kasance a cikinku, ku roƙi kome da kuke so, za a kuwa ba ku.
Wenn ihr in mir bleibt und meine Worte in euch bleiben, so mögt ihr bitten, um was ihr wollt, es wird euch zuteil werden.
8 Wannan ne yakan kawo ɗaukaka ga Ubana, ku ba da’ya’ya da yawa, kuna kuma nuna kanku ku almajiraina ne.
Dadurch wird mein Vater verherrlicht, daß ihr reiche Frucht bringt und meine Jünger werdet.
9 “Kamar yadda Uba ya ƙaunace ni, haka ni ma na ƙaunace ku. To, fa, ku kasance cikin ƙaunata.
Wie mich der Vater geliebt hat, so habe auch ich euch geliebt. Bleibt in meiner Liebe!
10 In kuka yi biyayya da umarnaina, za ku kasance a cikin ƙaunata, kamar dai yadda na yi biyayya da umarnan Ubana na kuma kasance a cikin ƙaunarsa.
Wenn ihr meine Gebote haltet, dann bleibt ihr in meiner Liebe, so wie auch ich die Gebote meines Vaters gehalten habe und in seiner Liebe bleibe.
11 Na gaya muku wannan domin murnata ta kasance a cikinku, murnanku kuma ta zama cikakkiya.
Das habe ich zu euch gesagt, damit meine Freude in euch sei und eure Freude vollendet werde.
12 Umarnina shi ne, Ku ƙaunaci juna kamar yadda na ƙaunace ku.
Das ist mein Gebot: Liebet einander, so wie ich euch geliebt habe.
13 Babu ƙaunar da ta fi wannan, a ce mutum ya ba da ransa saboda abokansa.
Niemand hat eine größere Liebe, als wer sein Leben einsetzt für seine Freunde.
14 Ku abokaina ne, in kun yi abin da na umarta.
Ihr seid meine Freunde, wenn ihr tut, was ich euch auftrage.
15 Ba zan ƙara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abin da maigidansa yake yi ba. A maimako in ce da ku abokai, domin na sanar da ku duk abin da na ji daga wurin Ubana.
Ich nenne euch nicht mehr Knechte; der Knecht weiß nicht, was sein Herr tut. Freunde habe ich euch genannt; denn ich habe euch alles geoffenbart, was ich von meinem Vater gehört habe.
16 Ba ku kuka zaɓe ni ba, a’a, ni ne na zaɓe ku na kuma naɗa ku ku je ku ba da’ya’ya-’ya’yan da za su dawwama. Uba kuwa zai ba ku duk abin da kuka roƙa cikin sunana.
Nicht ihr habt mich erwählt, sondern ich habe euch erwählt und euch bestellt, damit ihr hingeht und Frucht bringt und eure Frucht von Dauer sei, damit euch der Vater alles gebe, um was ihr ihn in meinem Namen bittet.
17 Umarnina ke nan. Ku ƙaunaci juna.
Nur dies ist mein Gebot: Liebet einander!
18 “In duniya ta ƙi ku, ku san cewa ta fara ƙin na ne.
Wenn die Welt euch haßt, bedenket, daß sie mich vor euch gehaßt hat.
19 Da ku na duniya ne, da ta ƙaunaci abinta. Kamar yadda yake, ku ba na duniya ba ne, na zaɓe ku daga duniya, shi ya sa duniya take ƙinku.
Ja, wäret ihr aus der Welt, so würde die Welt ihr Eigenes lieben. Da ihr aber nicht aus der Welt seid, vielmehr ich euch aus der Welt auserwählt habe, so haßt euch die Welt.
20 Ku tuna da kalmomin da na yi muku cewa, ‘Ba bawan da ya fi maigidansa,’In sun tsananta mini, ku ma za su tsananta muku. Da sun yi biyayya da koyarwata, da za su yi biyayya da taku ma.
Denkt an das Wort, das ich zu euch gesprochen habe: Ein Knecht ist nicht höher als sein Herr. Wenn sie mich verfolgt haben, so werden sie auch euch verfolgen; und haben sie mein Wort bewahrt, so werden sie auch das eurige bewahren.
21 Za su yi muku haka saboda sunana, gama ba su san Wannan da ya aiko ni ba.
Doch all dies werden sie um meines Namens willen euch antun, weil sie den nicht kennen, der mich gesandt hat.
22 Da a ce ban zo na yi musu magana ba, da ba su da zunubi. Yanzu kam, ba su da wata hujja a kan zunubinsu.
Wäre ich nicht gekommen und hätte nicht zu ihnen gesprochen, so hätten sie keine Sünde; nun aber haben sie für ihre Sünde keine Entschuldigung.
23 Wanda ya ƙi ni ya ƙi ya ƙi Ubana ma.
Wer mich haßt, haßt auch meinen Vater.
24 Da a ce ban yi ayyuka a cikinsu waɗanda babu wani da ya taɓa yi ba, da ba su da zunubi. Amma yanzu sun ga waɗannan ayyukan banmamaki, duk da haka sun ƙi ni sun kuma ƙi Ubana.
Hätte ich nicht Taten unter ihnen vollbracht, wie sie kein anderer vollbracht hat, dann hätten sie keine Sünde. Nun aber haben sie gesehen, und dennoch hassen sie mich und meinen Vater.
25 Amma wannan ya faru ne domin a cika abin da yake a rubuce cikin Dokarsu cewa, ‘Sun ƙi ni ba dalili.’
Aber das Wort, das in ihrem Gesetze steht, mußte in Erfüllung gehen: 'Sie haßten mich ganz ohne Grund.'
26 “Sa’ad da Mai Taimako ya zo, wanda zan aiko muku daga wurin Uba, Ruhun gaskiya wanda yake fitowa daga wurin Uba, zai ba da shaida game da ni.
Wenn dann der Beistand kommt, den ich euch vom Vater senden werde, der Geist der Wahrheit, der vom Vater ausgeht, so wird er Zeugnis über mich ablegen.
27 Ku ma dole ku ba da shaida, domin kun kasance tare da ni tun daga farko.
Auch ihr sollt Zeugnis ablegen, weil ihr von Anfang an bei mir seid,"

< Yohanna 15 >