< Yohanna 15 >

1 “Ni ne kuringar inabi na gaskiya, Ubana kuwa shi ne manomin.
Moi, je suis le vrai cep, et mon Père est le cultivateur.
2 Yakan sare kowane reshe a cikina da ba ya’ya’ya, amma yakan ƙundume kowane reshe da yake ba da’ya’ya, domin yă ƙara ba da’ya’ya.
Tout sarment en moi qui ne porte pas de fruit, il l’ôte; et tout sarment qui porte du fruit, il le nettoie, afin qu’il porte plus de fruit.
3 Kun riga kun zama masu tsabta saboda maganar da na yi muku.
Vous, vous êtes déjà nets, à cause de la parole que je vous ai dite.
4 Ku kasance a cikina, ni kuma zan kasance a cikinku. Babu reshen da zai iya yin’ya’ya da kansa, dole yă kasance a jikin kuringar inabin. Haka ku ma, ba za ku iya ba da’ya’ya ba sai kun kasance a cikina.
Demeurez en moi, et moi en vous. Comme le sarment ne peut pas porter de fruit de lui-même, à moins qu’il ne demeure dans le cep, de même vous non plus [vous ne le pouvez pas], à moins que vous ne demeuriez en moi.
5 “Ni ne kuringar inabin; ku ne kuma rassan. In mutum ya kasance a cikina ni kuma a cikinsa, zai ba da’ya’ya da yawa; in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
Moi, je suis le cep, vous, les sarments. Celui qui demeure en moi, et moi en lui, celui-là porte beaucoup de fruit; car, séparés de moi, vous ne pouvez rien faire.
6 Duk wanda bai kasance a cikina ba, yana kamar reshen da aka jefar yă bushe; irin waɗannan rassan ne akan tattara, a jefa cikin wuta a ƙone.
Si quelqu’un ne demeure pas en moi, il est jeté dehors comme le sarment, et il sèche; et on les amasse, et on les met au feu, et ils brûlent.
7 In kun kasance a cikina kalmomina kuma suka kasance a cikinku, ku roƙi kome da kuke so, za a kuwa ba ku.
Si vous demeurez en moi, et que mes paroles demeurent en vous, vous demanderez ce que vous voudrez, et il vous sera fait.
8 Wannan ne yakan kawo ɗaukaka ga Ubana, ku ba da’ya’ya da yawa, kuna kuma nuna kanku ku almajiraina ne.
En ceci mon Père est glorifié, que vous portiez beaucoup de fruit; et vous serez mes disciples.
9 “Kamar yadda Uba ya ƙaunace ni, haka ni ma na ƙaunace ku. To, fa, ku kasance cikin ƙaunata.
Comme le Père m’a aimé, moi aussi je vous ai aimés; demeurez dans mon amour.
10 In kuka yi biyayya da umarnaina, za ku kasance a cikin ƙaunata, kamar dai yadda na yi biyayya da umarnan Ubana na kuma kasance a cikin ƙaunarsa.
Si vous gardez mes commandements, vous demeurerez dans mon amour; comme moi j’ai gardé les commandements de mon Père, et je demeure dans son amour.
11 Na gaya muku wannan domin murnata ta kasance a cikinku, murnanku kuma ta zama cikakkiya.
Je vous ai dit ces choses, afin que ma joie soit en vous, et que votre joie soit accomplie.
12 Umarnina shi ne, Ku ƙaunaci juna kamar yadda na ƙaunace ku.
C’est ici mon commandement: Que vous vous aimiez les uns les autres, comme je vous ai aimés.
13 Babu ƙaunar da ta fi wannan, a ce mutum ya ba da ransa saboda abokansa.
Personne n’a un plus grand amour que celui-ci, qu’il laisse sa vie pour ses amis.
14 Ku abokaina ne, in kun yi abin da na umarta.
Vous êtes mes amis, si vous faites tout ce que moi je vous commande.
15 Ba zan ƙara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abin da maigidansa yake yi ba. A maimako in ce da ku abokai, domin na sanar da ku duk abin da na ji daga wurin Ubana.
Je ne vous appelle plus esclaves, car l’esclave ne sait pas ce que son maître fait; mais je vous ai appelés amis, parce que je vous ai fait connaître tout ce que j’ai entendu de mon Père.
16 Ba ku kuka zaɓe ni ba, a’a, ni ne na zaɓe ku na kuma naɗa ku ku je ku ba da’ya’ya-’ya’yan da za su dawwama. Uba kuwa zai ba ku duk abin da kuka roƙa cikin sunana.
Ce n’est pas vous qui m’avez choisi; mais c’est moi qui vous ai choisis et qui vous ai établis, afin que vous alliez, et que vous portiez du fruit, et que votre fruit demeure; afin que tout ce que vous demanderez au Père en mon nom, il vous le donne.
17 Umarnina ke nan. Ku ƙaunaci juna.
Je vous commande ces choses, c’est que vous vous aimiez les uns les autres.
18 “In duniya ta ƙi ku, ku san cewa ta fara ƙin na ne.
Si le monde vous hait, sachez qu’il m’a haï avant vous.
19 Da ku na duniya ne, da ta ƙaunaci abinta. Kamar yadda yake, ku ba na duniya ba ne, na zaɓe ku daga duniya, shi ya sa duniya take ƙinku.
Si vous étiez du monde, le monde aimerait ce qui serait sien; mais parce que vous n’êtes pas du monde, mais que moi je vous ai choisis du monde, à cause de cela le monde vous hait.
20 Ku tuna da kalmomin da na yi muku cewa, ‘Ba bawan da ya fi maigidansa,’In sun tsananta mini, ku ma za su tsananta muku. Da sun yi biyayya da koyarwata, da za su yi biyayya da taku ma.
Souvenez-vous de la parole que moi je vous ai dite: L’esclave n’est pas plus grand que son maître. S’ils m’ont persécuté, ils vous persécuteront aussi; s’ils ont gardé ma parole, ils garderont aussi la vôtre.
21 Za su yi muku haka saboda sunana, gama ba su san Wannan da ya aiko ni ba.
Mais ils vous feront toutes ces choses à cause de mon nom, parce qu’ils ne connaissent pas celui qui m’a envoyé.
22 Da a ce ban zo na yi musu magana ba, da ba su da zunubi. Yanzu kam, ba su da wata hujja a kan zunubinsu.
Si je n’étais pas venu, et que je ne leur aie pas parlé, ils n’auraient pas eu de péché; mais maintenant ils n’ont pas de prétexte pour leur péché.
23 Wanda ya ƙi ni ya ƙi ya ƙi Ubana ma.
Celui qui me hait, hait aussi mon Père.
24 Da a ce ban yi ayyuka a cikinsu waɗanda babu wani da ya taɓa yi ba, da ba su da zunubi. Amma yanzu sun ga waɗannan ayyukan banmamaki, duk da haka sun ƙi ni sun kuma ƙi Ubana.
Si je n’avais pas fait parmi eux les œuvres qu’aucun autre n’a faites, ils n’auraient pas eu de péché; mais maintenant ils ont, et vu, et haï et moi et mon Père.
25 Amma wannan ya faru ne domin a cika abin da yake a rubuce cikin Dokarsu cewa, ‘Sun ƙi ni ba dalili.’
Mais c’est afin que fût accomplie la parole qui est écrite dans leur loi: « Ils m’ont haï sans cause ».
26 “Sa’ad da Mai Taimako ya zo, wanda zan aiko muku daga wurin Uba, Ruhun gaskiya wanda yake fitowa daga wurin Uba, zai ba da shaida game da ni.
Mais quand le Consolateur sera venu, lequel moi je vous enverrai d’auprès du Père, l’Esprit de vérité, qui procède du Père, celui-là rendra témoignage de moi.
27 Ku ma dole ku ba da shaida, domin kun kasance tare da ni tun daga farko.
Et vous aussi, vous rendrez témoignage; parce que dès le commencement vous êtes avec moi.

< Yohanna 15 >