< Yohanna 15 >
1 “Ni ne kuringar inabi na gaskiya, Ubana kuwa shi ne manomin.
I am the true vine, and my Father is the vine-dresser.
2 Yakan sare kowane reshe a cikina da ba ya’ya’ya, amma yakan ƙundume kowane reshe da yake ba da’ya’ya, domin yă ƙara ba da’ya’ya.
Every branch in me that bears no fruit, he takes away; and every branch that bears fruit, he prunes, that it may bear more fruit.
3 Kun riga kun zama masu tsabta saboda maganar da na yi muku.
Now are you pure, through the word which I have spoken to you.
4 Ku kasance a cikina, ni kuma zan kasance a cikinku. Babu reshen da zai iya yin’ya’ya da kansa, dole yă kasance a jikin kuringar inabin. Haka ku ma, ba za ku iya ba da’ya’ya ba sai kun kasance a cikina.
Abide in me, and I will abide in you. As the branch can not bear fruit of itself, unless it abide in the vine, so neither can you, unless you abide in me.
5 “Ni ne kuringar inabin; ku ne kuma rassan. In mutum ya kasance a cikina ni kuma a cikinsa, zai ba da’ya’ya da yawa; in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
I am the vine, you are the branches. He that abides in me and I in him, he will bear much fruit; for apart from me you can do nothing.
6 Duk wanda bai kasance a cikina ba, yana kamar reshen da aka jefar yă bushe; irin waɗannan rassan ne akan tattara, a jefa cikin wuta a ƙone.
If any one abide not in me, he is thrown out as a branch, and withers; and such are gathered, and thrown into the fire, and burned.
7 In kun kasance a cikina kalmomina kuma suka kasance a cikinku, ku roƙi kome da kuke so, za a kuwa ba ku.
If you abide in me, and my words abide in you, you shall ask what you will, and it shall be done for you.
8 Wannan ne yakan kawo ɗaukaka ga Ubana, ku ba da’ya’ya da yawa, kuna kuma nuna kanku ku almajiraina ne.
In this is my Father glorified, that you bear much fruit; and in this you will be my disciples.
9 “Kamar yadda Uba ya ƙaunace ni, haka ni ma na ƙaunace ku. To, fa, ku kasance cikin ƙaunata.
As the Father has loved me, so have I loved you; abide in my love.
10 In kuka yi biyayya da umarnaina, za ku kasance a cikin ƙaunata, kamar dai yadda na yi biyayya da umarnan Ubana na kuma kasance a cikin ƙaunarsa.
If you keep my commandments, you shall abide in my love, even as I have kept my Father’s commandments, and abide in his love.
11 Na gaya muku wannan domin murnata ta kasance a cikinku, murnanku kuma ta zama cikakkiya.
These things have I spoken to you, that my joy may remain in you, and that your joy may be full.
12 Umarnina shi ne, Ku ƙaunaci juna kamar yadda na ƙaunace ku.
This is my commandment: That you love one another, as I have loved you.
13 Babu ƙaunar da ta fi wannan, a ce mutum ya ba da ransa saboda abokansa.
Greater love has no man than this, that one should lay down his life for his friends.
14 Ku abokaina ne, in kun yi abin da na umarta.
You are my friends, if you do whatever I command you.
15 Ba zan ƙara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abin da maigidansa yake yi ba. A maimako in ce da ku abokai, domin na sanar da ku duk abin da na ji daga wurin Ubana.
I no longer call you servants, because the servant knows not what his master does. But I have called you friends; for all things that I have heard from my Father, I have made known to you.
16 Ba ku kuka zaɓe ni ba, a’a, ni ne na zaɓe ku na kuma naɗa ku ku je ku ba da’ya’ya-’ya’yan da za su dawwama. Uba kuwa zai ba ku duk abin da kuka roƙa cikin sunana.
You have not chosen me, but I have chosen you, and appointed you, that you may go and bring forth fruit, and that your fruit may remain; that whatever you ask of the Father in my name, he may give you.
17 Umarnina ke nan. Ku ƙaunaci juna.
These things I command you, that you may love one another.
18 “In duniya ta ƙi ku, ku san cewa ta fara ƙin na ne.
If the world hates you, you know that it hated me before it hated you.
19 Da ku na duniya ne, da ta ƙaunaci abinta. Kamar yadda yake, ku ba na duniya ba ne, na zaɓe ku daga duniya, shi ya sa duniya take ƙinku.
If you were of the world, the world would love its own. But because you are not of the world, but I have chosen you out of the world, therefore the world hates you.
20 Ku tuna da kalmomin da na yi muku cewa, ‘Ba bawan da ya fi maigidansa,’In sun tsananta mini, ku ma za su tsananta muku. Da sun yi biyayya da koyarwata, da za su yi biyayya da taku ma.
Remember the word which I spoke to you, The servant is not greater than his master. If they have persecuted me, they will also persecute you; if they have kept my word, they will keep yours also.
21 Za su yi muku haka saboda sunana, gama ba su san Wannan da ya aiko ni ba.
But all these things they will do to you on my account, because they know not him that sent me.
22 Da a ce ban zo na yi musu magana ba, da ba su da zunubi. Yanzu kam, ba su da wata hujja a kan zunubinsu.
If I had not come and spoken to them, they would not have had sin; but now they have no excuse for their sin.
23 Wanda ya ƙi ni ya ƙi ya ƙi Ubana ma.
He that hates me, hates my Father also.
24 Da a ce ban yi ayyuka a cikinsu waɗanda babu wani da ya taɓa yi ba, da ba su da zunubi. Amma yanzu sun ga waɗannan ayyukan banmamaki, duk da haka sun ƙi ni sun kuma ƙi Ubana.
If I had not done among them the works that no other man has done, they would have had no sin; but now they have both seen, and hated both me and my Father.
25 Amma wannan ya faru ne domin a cika abin da yake a rubuce cikin Dokarsu cewa, ‘Sun ƙi ni ba dalili.’
But this is so, that the word may be fulfilled which is written in their law, They hated me without a cause.
26 “Sa’ad da Mai Taimako ya zo, wanda zan aiko muku daga wurin Uba, Ruhun gaskiya wanda yake fitowa daga wurin Uba, zai ba da shaida game da ni.
But when the Paraclete has come, whom I will send to you from my Father, the Spirit of the truth, which proceeds from the Father, he will testify of me;
27 Ku ma dole ku ba da shaida, domin kun kasance tare da ni tun daga farko.
and you also will testify, because you have been with me from the beginning.