< Yohanna 13 >

1 Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
Now before the feast of the Passover, Jesus, knowing that his time had come that he would depart from this world to the Father, having loved his own who were in the world, he loved them to the end.
2 Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
And during the meal, the devil had already put into the heart of Judas Iscariot, Simon's son, to betray him.
3 Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
Because he knew that the Father had given all things into his hands, and that he came forth from God, and was going to God,
4 saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
arose from the meal, and removed his outer garments. He took a towel, and wrapped a towel around his waist.
5 Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
Then he poured water into the basin, and began to wash the disciples' feet, and to wipe them with the towel that was wrapped around him.
6 Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
Then he came to Simon Peter. He said to him, "Lord, do you wash my feet?"
7 Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
Jesus answered him, "You do not know what I am doing now, but you will understand later."
8 Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn g165)
Peter said to him, "You will never wash my feet." Jesus answered him, "If I do not wash you, you have no part with me." (aiōn g165)
9 Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
Simon Peter said to him, "Lord, not my feet only, but also my hands and my head."
10 Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
Jesus said to him, "Someone who has bathed only needs to have his feet washed, but is completely clean. You are clean, but not all of you."
11 Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
For he knew him who would betray him, therefore he said, "You are not all clean."
12 Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
So when he had washed their feet, put his outer garment back on, and sat down again, he said to them, "Do you know what I have done to you?
13 Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
You call me, 'Teacher' and 'Lord.' You say so correctly, for so I am.
14 Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
If I then, the Lord and the Teacher, have washed your feet, you also ought to wash one another's feet.
15 Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
For I have given you an example, that you also should do as I have done to you.
16 Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
Truly, truly, I tell you, a servant is not greater than his master, neither one who is sent greater than he who sent him.
17 Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
If you know these things, blessed are you if you do them.
18 “Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
I do not speak concerning all of you. I know whom I have chosen. But that the Scripture may be fulfilled, 'He who ate my bread has lifted up his heel against me.'
19 “Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
I am telling you this now before it happens, so that when it does happen you may believe that I am he.
20 Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
Truly, truly, I tell you, he who receives whomever I send, receives me; and he who receives me, receives him who sent me."
21 Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
When Jesus had said this, he was troubled in spirit, and testified, "Truly, truly, I tell you that one of you will betray me."
22 Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
The disciples looked at one another, perplexed about whom he spoke.
23 Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
One of his disciples, whom Jesus loved, was reclining against Jesus' chest.
24 Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
Simon Peter therefore motioned to him to inquire who it was he was talking about.
25 Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
He, leaning back, as he was, on Jesus' chest, asked him, "Lord, who is it?"
26 Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
Jesus therefore answered, "It is he to whom I will give this piece of bread when I have dipped it." So when he had dipped the piece of bread, he gave it to Judas, the son of Simon Iscariot.
27 Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
After the piece of bread, then Satan entered into him. Then Jesus said to him, "What you do, do quickly."
28 Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
Now none of those reclining knew why he said this to him.
29 Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
For some thought, because Judas had the money box, that Jesus said to him, "Buy what things we need for the feast," or that he should give something to the poor.
30 Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
Therefore, having received the piece of bread, he went out immediately; and it was night.
31 Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
When he had gone out, Jesus said, "Now the Son of Man has been glorified, and God has been glorified in him.
32 In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
If God has been glorified in him, God will also glorify him in himself, and he will glorify him at once.
33 “’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
Little children, I will be with you a little while longer. You will seek me, and as I said to the Jewish leaders, 'Where I am going, you cannot come,' so now I tell you.
34 “Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
A new commandment I give to you, that you love one another. Just as I have loved you, you also must love one another.
35 Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
By this everyone will know that you are my disciples, if you have love for one another."
36 Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
Simon Peter said to him, "Lord, where are you going?" Jesus answered, "Where I am going, you cannot follow now, but you will follow afterwards."
37 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
Peter said to him, "Lord, why can I not follow you now? I will lay down my life for you."
38 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!
Jesus answered him, "Will you lay down your life for me? Truly, truly, I tell you, the rooster won't crow until you have denied me three times.

< Yohanna 13 >