< Yohanna 13 >
1 Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
Před svátkem pak velikonočním, věda Ježíš, že přišla hodina jeho, aby šel z tohoto světa k Otci, milovav své, kteříž byli na světě, až do konce je miloval.
2 Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
A když večeřeli, (a ďábel již byl vnukl v srdce Jidáše Šimona Iškariotského, aby jej zradil, )
3 Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
Věda Ježíš, že jemu Otec všecko v ruce dal, a že od Boha vyšel a k Bohu jde,
4 saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
Vstal od večeře, a složil roucho, a vzav rouchu, přepásal se.
5 Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
Potom nalil vody do medenice, i počal umývati nohy učedlníků a vytírati rouchou, kterouž byl přepásán.
6 Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
Tedy přišel k Šimonovi Petrovi, a on řekl jemu: Pane, ty mi chceš nohy mýti?
7 Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
Odpověděl Ježíš a řekl jemu: Co já činím, ty nevíš nyní, ale potom zvíš.
8 Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn )
Dí jemu Petr: Nebudeš ty mýti noh mých na věky. Odpověděl jemu Ježíš: Neumyji-liť tebe, nebudeš míti dílu se mnou. (aiōn )
9 Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
Dí jemu Šimon Petr: Pane, netoliko nohy mé, ale i ruce i hlavu.
10 Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
Řekl jemu Ježíš: Kdož jest umyt, nepotřebuje, než aby nohy umyl; nebo čist jest všecken. I vy čisti jste, ale ne všickni.
11 Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
Nebo věděl o zrádci svém; protož řekl: Ne všickni čisti jste.
12 Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
Když pak umyl nohy jejich, a vzal roucho své, posadiv se za stůl zase, řekl jim: Víte-liž, co jsem učinil vám?
13 Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
Vy nazýváte mne Mistrem a Pánem, a dobře pravíte, jsemť zajisté.
14 Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
Poněvadž tedy já umyl jsem nohy vaše, Pán a Mistr, i vy máte jeden druhému nohy umývati.
15 Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
Příklad zajisté dal jsem vám, abyste, jakož jsem já učinil vám, i vy činili.
16 Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
Amen, amen pravím vám: Není služebník větší nad pána svého, ani posel větší nežli ten, kdož jej poslal.
17 Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
Znáte-li tyto věci, blahoslavení jste, budete-li je činiti.
18 “Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
Ne o všechť vás pravím. Já vím, které jsem vyvolil, ale musíť se naplniti písmo: Ten, kdož jí chléb se mnou, pozdvihl proti mně paty své.
19 “Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
Nyní pravím, vám, prvé než by se stalo, abyste, když se stane, uvěřili, že já jsem.
20 Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
Amen, amen pravím vám: Kdo přijímá toho, kohož bych já poslal, mneť přijímá; a kdož mne přijímá, přijímá toho, kterýž mne poslal.
21 Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
A to pověděv Ježíš, zkormoutil se v duchu, a osvědčil, řka: Amen, amen pravím vám, že jeden z vás mne zradí.
22 Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
Tedy učedlníci vzhlédali na sebe vespolek, pochybujíce, o kom by to pravil.
23 Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
Byl pak jeden z učedlníků Ježíšových, kterýž zpolehl na klíně jeho, ten, jehož miloval Ježíš.
24 Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
Protož tomu návěští dal Šimon Petr, aby se zeptal, kdo by to byl, o němž praví.
25 Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
A on odpočívaje na prsech Ježíšových, řekl jemu: Pane, kdo jest?
26 Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
Odpověděl Ježíš: Ten jest, komuž já omočené skyvy chleba podám. A omočiv skyvu chleba, podal Jidášovi, synu Šimona Iškariotského.
27 Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
A hned po té skyvě chleba vstoupil do něho satan. I řekl jemu Ježíš: Co činíš, čiň spěšně.
28 Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
Tomu pak žádný z přísedících nerozuměl, k čemu by jemu to řekl.
29 Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
Nebo někteří se domnívali, poněvadž Jidáš měšec měl, že by jemu řekl Ježíš: Nakup těch věcí, kterýchž jest nám potřebí k svátku, aneb aby něco chudým dal.
30 Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
A on vzav skyvu chleba, hned vyšel, A byla noc.
31 Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
Když pak on vyšel, dí Ježíš: Nyníť oslaven jest Syn člověka, a Bůh oslaven jest v něm.
32 In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
A poněvadž Bůh oslaven jest v něm, i Bůh oslaví jej sám v sobě, a to hned oslaví jej.
33 “’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
Synáčkové, ještě maličko s vámi jsem. Hledati mne budete, ale jakož jsem řekl Židům: Kam já jdu, vy nemůžete přijíti, i vám pravím nyní.
34 “Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
Přikázaní nové dávám vám, abyste se milovali vespolek; jakož já miloval jsem vás, abyste i vy milovali jeden druhého.
35 Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
Po tomť poznají všickni, že jste moji učedlníci, budete-li míti lásku jedni k druhým.
36 Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
Dí jemu Šimon Petr: Pane, kam jdeš? Odpověděl mu Ježíš: Kam jdu, nemůžeš ty nyní jíti za mnou, ale půjdeš potom.
37 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
Dí jemu Petr: Pane, proč bych nemohl nyní jíti za tebou? Duši svou za tebe položím.
38 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!
Odpověděl jemu Ježíš: Duši svou za mne položíš? Amen, amen pravím tobě: Nezazpíváť kohout, až mne třikrát zapříš.