< Yohanna 13 >
1 Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
Lätnak Pawi a pha vai mhnüp mat a hlü ham üng, Jesuh naw hina khawmdek ceh ta lü Paa veia a cehnak vai kcün pha lawki ti ksingki. Hina khawmdeka veki a khyange cen aläa jah mhläkphyanak lü adüt vei cäpa jah kphyanaki.
2 Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
Jesuh ja axüisaw he naw mü buh eikie. Sihmona capa, Judaha mlung k’uma, Jesuh phyehei khaia khawyai naw a mhlawmcawk pänga kyaki.
3 Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
Pa naw ahmäi a mhjum ja Mhnam üngkhyüh law lü Pamhnama veia cit be khai ti cun Jesuh naw ksingki.
4 saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
Acunakyase, buh capawi üngka naw tho law lü a jih ngvaih sut lü ngxuheinak jih a vawh.
5 Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
Kbe ksung üng tui kyäi lü axüisaw hea khaw jah mthih pet lü a jih vawh am a jah xuh pet.
6 Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
Sihmon Pita veia a pha law üng, “Bawipa aw, ka khaw na na mthih hlü petki aw?” a ti.
7 Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
Jesuh naw, “Tukbäih i ka pawhmsah ti am ksing hamki; acunsepi, tuha ta na ksing law khai ni” ti lü a msang.
8 Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn )
Pita naw, “Ka khaw käh na mthi sümsüm khai” a ti. Jesuh naw, “Na khaw am ka ning mthih pet üng ta keia hnukläka am kya tiki” a ti. (aiōn )
9 Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
Sihmon Pita naw, “Bawipa aw, acun ani üng ta ka khaw däk am ni lü ka kut ja ka lu pi na mthih peta” a ti.
10 Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
Jesuh naw, “Tui nghlawk pängki naküt ngcimki ni, i a mthih vai am hlü, a khaw däk ni a hlü. Nangmi avan ngcimcaih päng ve uki, acunsepi am ngcimcaih hamki mat ve ve” a ti. (
11 Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
U naw jawiei khai a ksing pänga phäha, “Nami van nami ngcimki, lüpi am ngcimki mat nami ksunga veki” a ti.)
12 Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
Ami khaw jah mthih pet lü, a jih ngvaih be lü, ngaw beki naw, “Nami khana ka pawh hin asuilam nami ksingki aw?
13 Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
“Nangmi naw Saja aw, Bawipa aw nami na ti na khawiki. Nami cangki, ka kya kungki.
14 Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
“Kei nami na Bawipa ja Saja hngawh naw nami khaw ka ning jah mthih pet üng, nangmi pi mat naw mata khaw nami mthih pet vai.
15 Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
“Nami khana ka pawha mäiha nangmi naw pi nami pawh hnga vaia ka ning jah mhnuhki.
16 Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
“Akcanga ka ning jah mtheh ta: mpya cen a mahpa kthaka am däm bawk khawi; ngsäe cun pi jah tüihkia kthaka däm bawkia am kya.
17 Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
“Ahina ngthungtak nami ksingki, nami ksinga mäiha nami xünpüi üng ta ihlawka nami jo sen khai ni.
18 “Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
“Nami vana mawng ka pyen am ni. Ka xüe ka jah ksingki. Acunsepi, ‘Kani ei yümki naw am na ngja hlü ve’ ti lü, cangcima kümkawi lawnak vaia kyaki.
19 “Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
“Ahin hin am a pha law ham üng, atuh ka ning jah mtheh ni. Acun a pha law üng ‘Kei Ania Ka Kyaki’ ti nami jumnak thei vaia ka ning jah mtheh ni.
20 Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
“Akcanga ka ning jah mthehki: au pi ka tüi law dokhameiki cun kei na dokhameiki ni; au pi ka tüi law dokhamki naw, kei pi na dokhameikia kyaki. Kei na dokhameiki naw pi na tüi lawki dokhamkia kyaki” ti lü a pyen.
21 Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
Jesuh naw acukba a pyen law päng üng a mlung khuikha lü, “Akcanga ka ning jah mthehki: nangmi üngka mat naw na phyehei khai” ti lü a jah mtheh.
22 Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
U a pyennak hman am ksing u lü axüisaw he naw ami püi ci teng lü awmki he.
23 Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
Axüisawe üngka mat, Jesuha kphyanak cun Jesuha peia ngawki.
24 Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
Sihmon Pita naw, “U a pyenak ni, na mtheha” ti lü, a kut am khiktawt hü lü a kthäh.
25 Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
Acuna axüisaw naw Jesuh peia va ngnawn lü, “Bawipa aw, u ni?” a ti.
26 Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
Jesuh naw, “Hina muk mte mcawi lü ka peta khyanga kya khai” ti lü a msang. Muk mte mcawi lü, Sihmona capa Judah üng a pet.
27 Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
Muk mte a doei ja khawyam a k’uma lutki. Jesuh naw, “Na pawh vai akjanga pawha” a ti.
28 Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
Ei kbe kunga ngawkie naw, i a pyennak ti, u naw pi am ksing u.
29 Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
Avang naw Judah Iskarot naw nguiip a cüma phäh, Jesuh naw, ‘‘Hina pawi üng mi summang vai va khyeia a tinak ni, am ani üng khuikha si mpyaki he üng ik’eih jah pea” tikia, ami ngai.
30 Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
Judah naw muk mte lo lü cit ktäihki. Acun cun mthana kyaki.
31 Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
Acukba a ceh käna Jesuh naw pyen lü, “Atuh hin Khyanga Capa mhlünmtaia kya ve. Ani üngkhyüh Pamhnam pi mhlünmtaia kya ve.
32 In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
“Ani üngkhyüh Pamhnama hlüngtainak mdan lü, Pamhnam naw Khyanga Capa pi amät üng mhlünmtai khai. Sängsäng se Pamhnam naw ani mhlünmtai khai.
33 “’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
“Ka canae aw, nami hlawnga ka ve vai hin am hjo ti. Nami na sui hü khaie. Acunüng, Judah ngvaie üng, ‘Ka cehnak vaia am law thei uki’ ti lü ka pyena mäiha atuh pi acukba bäa ka ning jah mthehki.
34 “Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
“Ngthumkhän kthai ka ning jah peki: mat ja mat mhläkphya na ua. Ka ning jah mhläkphyanaka mäiha mat ja mat mhläkphya na u.
35 Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
“Mat ja mat nami mhläkphyanak üng ta, khyang naküt naw ka hnukläke tia ning jah ksing khaie” a ti.
36 Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
Sihmon Pita naw, “Bawipa aw, hawia na cit khai?” a ti. Jesuh naw, “Ka cehnak hlüa nang tuh am law theiki; tuha ta na law thei khai” ti lü, a msang.
37 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
Pita naw, “Bawipa aw, ise atuh na hlawnga am ka law theiki ni? Na phäha ta thih vai pi am kyüh nawng” a ti.
38 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!
Jesuh naw, “Keia phäha na thih vai akcanga am na kyühki aw? Akcanga ka ning mthehki: nang naw ainghlüi am khawng ham se, ani am ksing ngü ti lü kthum vei na ngcim khai” a ti.